Monday 14 October 2024

Abubuwan Da So Yake Korewa

Abubuwan Da So Yake Korewa

So, a wani lokacin ya kore hankali sai ya tabbatar da hauka. Wani lokacin kuma ya kore hauka ya tabbatar da hankali.

Abubuwan Da So Yake Korewa 
Hoto: Adil Azeem/Pinterest

Marubuci:- Idris M Rismawy


So, shi ne yake kore abin da yake anan, kuma wani lokacin ya tabbatar da abun da babu shi.

Gane waɗannan kalaman sai waɗanda Allah ya nufa.

Saturday 12 October 2024

Yadda Za Ku Sauya Rayuwar Ku A Rabin Shekara Kacal  (2)

Yadda Za Ku Sauya Rayuwar Ku A Rabin Shekara Kacal (2)

Mun fara bayani a kan matakai goma da za su canza rayuwarka a cikin wata 6. Mun tattauna daga matakai na 1 zuwa na 3. Ya kamata mai karatu ya maida hankali a nan sosai, saboda a nan babban aiki yake.


Yadda Za Ku Sauya Rayuwar Ku A Rabin Shekara Kacal
Hoto: Protofuse

4. Ka canza wani abu da kake yi a kullum.


Masana suna cewa sirrin nasararka yana ɗauke a cikin tsarin yininka/wuninka (daily routine).


Bi ma'ana abin da kake yi kullum a rayuwarka daga safiya zuwa dare.


Ka tambayi kanka mana, ta yaya kake tafiyar da lokacinka, daga farkawarka daga barci har zuwa lokacin komawa shimfiɗarka?


Lokaci kam babu mai ja da muhimmancinsa saboda Allah da kanSa ya rantse da shi fiye da sau 10 a cikin Alƙur'ani Mai girma.


Allah ya rantse da Alfijir, Ya rantse da lokacin Asuba, Ya rantse da lokacin hantsi, Ya rantse da yini/wuni, da kuma dare, sannan Ya rantse da zamani gabaɗayansa.


To amma ta yaya za ka gano abin da za ka canza na tsarin yininka/wuninka?


Ka koma ka binciki waɗannan abubuwan:


1. Matsalolinka da ka zayyano a mataki na farko, da....


2. Manufofin da ka ayyana a mataki na biyu da kuma...


3. Abubuwan da suke shagaltar da kai da ka lissafa a mataki na uku (No.3).


Idan ka gano waɗanan gabaɗaya, to akwai wani GAGARUMIN AIKI a gabanka.


A nan ne za ka yi amfani da wani tsari na Rusau da Ginau mai muhimmanci.


RUSAU


1. Ka rusa, ka zare, ka goge, ka gusar, ka kawar da duk wata ɗabi'a, ko hali, ko shagala, ko yanayi, ko aiki, ko mutumin da ba ya ƙarfafa ka wurin isa ga burinka da ka ayyana a lamba ta 2.


A wannan matakin, za ka rabu da abokai da kuke zaman banza tare da su ba kwa tattauna wani abu na ci-gaba ko fa'ida a rayuwa.


Za ka rabu da budurwa/saurayi da kuke yaudarar juna, kuna ɓatawa juna lokaci da rayuwa alhali kun sani sarai ba auren juna za ku yi ba.


Za ka rabu da kallon fim, ko ka ba shi hutu, za ka rage hawa kan shafukan sada zumunta, idan so samu ne ma ka goge manhajojin (Apps) daga wayarka sai wanda ya zame maka tilas.


Idan ya zama dole sai ka hau shafukan sada zumunta don wani dalili, 


To ya zama dole ka yi;


- "unfollowing"


- ko "blocking"


- ko "unfriending" duk wani mutum ko shafi da ba ya bada gudunmawa wurin ci-gaban kanka da tunaninka, da sana'arka, ko iliminka, ko imaninka, ko auratayyarka da sauransu.


Dole ki yi blocking duk wani shashasha da bai san ciwon kansa ba yake zuwa inbox yana damunki da saƙonni na shiririta da shirme. Yin hakan taimakon kanki ne da ma shi kansa.


Dole ne ka rabu ka ja da baya da masu kashe maka gwiwa a kan manufofinka waɗanda komai ka ɗauko sai su ce maka ba zai yiwu ba.


Dole ki nisanta kanki daga duk wata ƙawa ko 'yan uwa masu kashe miki gwiwa akan sana'arki ko kasuwanciki ko aikin hannunki da kike rufawa kanki asiri a sanadinsa.


GINAU 


Idan ka kawar da dukkan waɗannan sai ka musanya su da ɗabi'u, da halaye, da ayyuka, da mutane masu taimakonka da ba ka ƙarfin gwiwa.


Amma kamar yadda na faɗa a baya, mutane da yawa ba za su iya wuce wannan matakin ba.


Sun gwammace su ci-gaba da wanzuwa a cikin yanayin da suke na rashin ma'ana, da salwantar da lokaci, da kasancewa tare da mutane masu hana su ci-gaba, da kuma riƙo da munanan ɗabi'unsu masu wuyar bari.


Idan ba za ka iya samar wa kanka da sauyin da rayuwarka take buƙata ba, za ka ci-gaba da rayuwa ne a cikin nadama.


Shi yasa muka yi alƙawarin yin bayani a kan wasu dodanni da dole mutum ya yaƙa domin wuce wannan matakin.


Su ne kamar haka:


1. Sabo


Na farkonsu kuma mafi illa a cikinsu shi ne sabo, wato abin da rai ko jiki ko zuciya ta saba da shi tsawon wata da watanni ko ma shekaru, rabuwa da shi ya kan yi mata matuƙar wahala.


Don haka dodo na farko kuma yaƙi na farko da za ka gwabza shi ne ka yaƙi kanka da kanka.


Ka ɗauka kamar mutum ne kai wanda ya daɗe yana cin wani abinci mai daɗin gaske amma kuma yana ɗauke da guba a ciki.


Shin daɗin wannan abincin da tsawon lokacin da ka ɗauka kana cin shi dalili ne da zai sa ka bar abincin ya kashe ka?


2. Tsoro


Dodo na biyu shi ne tsoro.


Shin hakan ma zai yiwu kuwa?


Shin zan iya yin nasara? Zan iya rayuwa idan babu wane da wance?


Akwai wani babban mutum da ya taɓa yin wata magana wacce har ila yau ta tsaya mini a rai. Yana cewa, "Mutane da yawa ba gazawa (failure) suke tsoro ba, nasara (success) suke tsoro."


Sai ka ga mutum cikin tsananin talauci ko sisi ba ya da shi, amma idan ka kawo masa wata dama ta aiki ko sana'a sai tsoro duk ya bi ya kame/kama shi.


Shin akwai wani abun tsoro ne dama da talauci, amma yin kuɗi yake tsoro ba talauci ba.


Mutum yana soyayya da wata tana matuƙar cutar da shi, ko yana wulaƙanta ta idan mace ce, amma yana ko tana tsoron rabuwa da su.


Za mu ci-gaba Insha Allah.


Tushe/Asali: Hausa Motivation 

Friday 11 October 2024

Gajeren Sakon Budurwa Na Soyayya Ga Saurayin Ta

Gajeren Sakon Budurwa Na Soyayya Ga Saurayin Ta

Ina son ka tamkar yadda ba zan iya bayyana maka ba. Ina sonka tamkar yadda ba za ka iya ƙirga adadin ruwan sama ba.


Saƙon Budurwa Na Soyayya Ga Saurayin Ta
Hoto: Dr. Jim Collins

Marubuci:- Abba Rabi'u


Ɗawainiya nake da son ka a cikin zuciyata, da sannu za ka fahimci ni masoyiyarka ce ta haƙiƙa.


Kada ka zubar da hawayenka, yayin da wani ya ɓata maka rai, tuna da wacce kake so, kake kuma ƙauna, sai zuciyarka ta yi fari.


Na zana zanen fulawar so a tafin hannuna na yi nufin nuna maka domin ka fahimci yanayin matsayin da son ka ya yi a cikin zuciyata.

Sirrin Yadda Ake Kirkirar Sana'o'i Masu Kawo Riba Sosai

Sirrin Yadda Ake Kirkirar Sana'o'i Masu Kawo Riba Sosai

Ina da shawara ta ƙirƙirar sabuwar sana'a, yaya zan fara? Ka daidaita wannan shawara da kadarorin da kake da su a ƙasa. Misali, idan ka san yadda ake ɗinki, to sai ka yi tunanin wani sabon salo da tsarin ɗinka kaya ta yin amfani da shago da kuma keken ɗinkin wani wanda kake mutunci da shi, ko ya ba ka haya, har sai ka samu ƙwarewa, da fahimtar kasuwa da kuɗaɗen da za su ishe ka sayo naka keken. Kar ka yi garajen kama ƙaton shago da sayo kayan aiki nan take. 


Sirrin Yadda Ake Kirkirar Sana'o'i Masu Kawo Riba Sosai
Hoto: Getty Images

MarubuciBello Galadanchi


Ka fara da 'yar ƙaramar sana’a, sai ka girma a tsanake. Ka kashe kuɗaɗen da ba za ka gurgunce ba idan sana’ar ta karye, ko kuma albashin da kake samu na watanni uku a shekara.


Hakan zai ba ka damar gwada wannan sabuwar sana’a, ta yadda idan ka samu akasi, to ba za ka karye baki ɗaya ba, kuma za ka iya yin nazarin kuskuren da ka yi, sai ka sake gwadawa. 


Idan kana da fasaha, to kar ka ƙirƙiri abu daga farko, idan har akwai irin shi a kasuwa. Ka sayo na kasuwar, sannan ka nazarce shi, kuma ka yi tunanin yadda za ka inganta shi. Idan ka yi sa’a kuma ka samu alheri bayan inganta na kasuwa, to daga nan kuma za ka iya zuba jari mai tsoka domin ƙirƙirar naka sabon salon, a dai-dai lokacin da kake ci-gaba da samun kuɗaɗen shiga daga tsohon salon.


Ka zama kana da tarko mai inganci, yadda idan tsuntsun ya ƙwace, to ba zai gudu da tarkonka ba.

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (4)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (4)

Lokacin da Laila ta kufce/kuɓce daga hannun mahaifiyarta kaitsaye sai ta ruga izuwa rabin ranta wato Kays Majnun kenan wanda yake kwance a sume sakamakon ƙunci da rashin ƙarfin jiki da ke addabarsa.


Ainihin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila
Hoto: Hamidsamejo

Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Tana isa gare shi sai ta durƙushe tana kuka gami da ambaton sunansa cikin wata murya mai ɗauke da sautin tausayi, shiru Majnun bai ko motsa ba balle ta sa ran zai amsa mata kiran nata, cikin shashsheƙar kuka Laila ta fara rerawa masoyinta wasu baitoci irin na masoya:


"Idaniyata tana ta zubar da ruwan hawaye.


Tafiyata ta zama tamkar ta masu maye.


Ga idanuwana a buɗe har gari ya waye.


Zuciyata ta soye.


Ka taso na gan ka rabin raina........."


Ganin har yanzu masoyin nata bai farfaɗoba sai zuciyarta ta karye, jikinta ya yi sanyi nan take ta faɗi a wajen da kalmar Majnun a bakinta.


A haka iyayen Lailar suka ƙaraso wajen da suke, suka ɗauke ta suka tafi da ita, suka bar Majnun kwance a sume a wajen.


Wata iska ce mai ƙarfin gaske ta ringa kaɗawa a ilahirin dajin da Majnun yake kwance, jim kaɗan da fara iskar kuma sai yanayin garin gabadaya ya canza kala, wanda hakan yake nuna cewa ruwan sama na gaf da sauka. Ruwan saman da ya fara sauka da ƙarfin gaske shi ne ya zamo silar farfaɗowar Majnun daga dogon suman da ya yi, yana farfaɗowa ya fara da kiran Laila!


Da rarrafe da jan jiki Majnun ya samu ya koma jikin bishiyar da yake ƙarƙashin ta dan dai ya tsira daga dukan ruwan saman, wasu zafafan hawaye ne suke sintiri daga ƙwayar idanunsa zuwa kan kumatunsa, gabadaya duniyar ta yi masa zafi gami da duhu, shin a ina zai ga Lailarsa ne? Me ya sa mutane suke masa kallon mahaukaci saboda kawai ya zurfafa a begen masoyiyarsa, me ya sa iyayen Laila ba sa jin tausayinsa ne? 


A haka ya kasance yana ta kuka da sambatu na rashin sanin ina zai ga Lailarsa har ruwan saman ya ɗauke, yana nan zaune sai ga wasu Fatake za su wuce sai suka ga Majnun kamar wani tsohon mahaukaci saboda gabaɗayansa ya canza kamar ba mutum ba. Fataken suka tsaya domin taimaka masa, Majnun ya kwashe labarinsa kaf shi da masoyiyarsa ya labartawa waɗannan fataken, koda fataken nan suka ji wannan labarin nasu sai suka cika da mamaki gami da tausayi, da yawa daga cikinsu suka ringa kuka saboda tsabar tausaya masa.


Majnun ya nemi fataken da su ba shi aron alƙalami da takarda zai rubutawa masoyiyarsa wasiƙa ya ba su su tafi da ita ko Allah zai sa su samu labarinta.


Suka amince da hakan kuma suka ba shi abin rubutu da takarda, ya karɓa ya fara rubutawa masoyiyarsa wasiƙa kamar haka:


"Zuwa ga wacca jin daɗin raina ya rataya a cikin ƙwayar idanunta, ki sani cewa Majnun ɗinki ba zai iya rayuwa ba idan ba da ke ba, zuciyata ta kurumce ba ta ji kuma ba ta gani matuƙar dai ni da ke za mu ci gaba da rayuwa a ware, ina mai baƙin cikin sanar da ke cewa ruhina yana gaf da barin gangar jikina mutuƙar dai na ɗau lokaci ban gan ki a kusa da ni ba Laila! Ki sani ya ke wadda farin cikina yake kai kawo a tare da ke ba zan gusa daga inda kika bar ni ba har sai ajalina ya riskeni a wajen". 


Bayan Majnun ya gama rubuta wasiƙar sai ya matsa can ƙasan wasiƙar ya rubuta wasu baitoci masu tsuma zuciyar duk wanda ya ji su:


"Yaushe ne za mu gana na ji sautin muryarki?


Zuciya sai tai ta kuka idan na duba ban gan ki ba.


A rayuwa idan babu ke ban san ni yaya zan yi ba.


Ina son jin kalamanki, ki ambata su gare ni ko zan samu haiba.


Ina ta kukan rashinki, ki tausaya min ki zo ki duba.


Ni da ke nake alfahari, Laila ki taho gare ni na bar ƙuncin zuciya......"


Fatake suka yi sallama da Majnun, fuskokinsu cike da tausayinsa, kuma suka yi masa alƙawarin Insha'Allahu za su sada wasiƙarsa ga masoyiyar tasa.


Bayan iyayen Laila sun tafi da ita, da suka isa masaukinsu sai aka yayyafa mata ruwa ta farfaɗo, tana farfaɗowa ta fara kuka gami da ambaton sunan Majnun, hankalin iyayenta ya tashi ganin ita ma ta fara bayyana duk wasu alamomi da Majnun ɗin yake nunawa a kanta, wato alamun hauka.


Iyayen Laila suka yanke shawara a kan su nufi can wajen ƙasar Bagadada domin yin ƙaura gabadaya daga yankin da 'yarsu za ta kuma ganin Majnun.


Nan da nan suka haɗa kayansu sai Bagadada, yayinda ita kuma Laila take kwance cikin matsananciyar rashin lafiya.


Kwanci tashi Fataken nan masu ɗauke da wasiƙar Majnun zuwa ga masoyiyarsa suka iso wani wuri wanda nan ne mahadar Fatake, daga wannan mahaɗar zuwa cikin ƙasar Habasha tafiya ce ta rabin kwana, wannan ne ya sa duk waɗanda suka zo da zummar shiga ƙasar Habasha sai sun tsaya a wannan mahaɗar domin kinkintsawa.


Jikin Laila sai ƙara tsananta yake, hakan ne yasa tafiyar tasu ba ta sauri, a hakan su ma suka samu suka iso wannan mahaɗar, a wannan mahaɗar suka yada zango kuma suka duƙufa nemawa 'yarsu magani, suka bada cigiya a wannan mahaɗar ko akwai mai maganin da zai iya warkar da 'yarsu, suka alƙawarta dukiya mai tarin yawa ga duk wanda ya yi nasarar warkar da ita, a shelar da aka yi sai karaf a kunnuwan waɗannan Fataken, wato waɗannan waɗanda suka ba wa Majnun magani, don haka jin an ce za a bada dukiya mai yawa sai suka je suka ce za su gwada warkar da Laila ɗin, yayin da aka kai su inda Lailar take sai aka labarta musu dalilin rashin lafiyartata.


Suna jin haka sai suka gane cewa lallai ita ce wadda Majnun ya labarta musu ita.


Fataken suka nemi da a bar su daga su sai ita a ɗakin domin a cewarsu akwai ma shafar jinni/aljanu a tare da ita, bayan an bar su daga su sai ita, sai suka labarta mata labarin masoyinta Majnun, nan da nan sai ta tashi zaune jin an ambaci Majnun ɗinta, bayan ta gama karanta wasiƙar da Majnun ya aiko mata da ita sai ta fashe da kuka, kuka mai ratsa zuciyar mai sauraro, anan Fataken suka rarrasheta da ƙyar sannan suka kwatanta mata nahiya da kuma wurin da suka baro masoyin nata.


Lokacin da iyayen Laila suka dawo ɗakin sai suka tarar da 'yarsu har ma ta tashi zaune kuma ga fara'a a fuskarta, nan take iyayenta suka nuna farin cikinsu sannan suka kawo dukiya mai tarin yawa suka ba wa Fataken nan kamar yadda suka alƙawarta.


Bayan kwana biyu da samun lafiyar Laila sai iyayenta suka yanke shawarar haɗa kayansu domin shiga cikin ƙasar Habasha, a lokacin da suka gama shirinsu kaf domin fara tafiyar, a lokacin ne kuma Laila ta sulale da taimakon wani mutum da ya sata a hanya kana ya samo mata doki ta bar nahiyar da nufin isa ga masoyinta, masoyinta na gaske wanda take da tabbacin har abada ba za a samu masoyi kamarsa ba.


Kwanci tashi, ta yada zango anan ta yada zango a can har ta shigo nahiyar da Majnun ɗinta yake, don haka sai ta ƙara ƙaimi domin ta kai ga rabin ran nata, gabaɗaya kamanninta ya sauya, tayi futu-futu da ita, kuma ta rame da ma kuma gashi ba ta daɗe da farfaɗowa daga rashin lafiya ba.


Za mu ci-gaba Insha Allah.

Thursday 10 October 2024

Yadda Za Ku Sauya Rayuwar Ku A Rabin Shekara Kacal  (1)

Yadda Za Ku Sauya Rayuwar Ku A Rabin Shekara Kacal (1)

Dakata ɗan uwa! Kamar jiya muka shiga shekarar 2024 amma ga shi har mun cinye rabinta. Shin za ka iya bugun ƙirji ka ce ga wani buri da ka cimma tsakanin farkon wannan shekarar zuwa yanzu? Idan babu, to lallai ka zauna ka yi wa kanka faɗa.


Sauya Rayuwar Ku A Rabin Shekara Kacal
Hoto: iStock Photo

Mutane da dama sun taɓa tsintar kansu a irin wannan yanayin amma suka cimma nasara. Don haka ruwa bai ƙare wa ɗan kada ba tukunna.


In dai ka shirya canza rayuwarka, akwai hanyoyi da za su taimake ka a kan yin hakan.


Waɗannan matakan guda goma da za mu kawo za su taimake ku wajen samun sauyi mai inganci a rayuwarku.


1. Ka fahimci rayuwarka (Clarity).


Hausawa suna cewa: " Mai ɗaki shi ya san inda ke masa yoyo."


Mataki na farko kuma mafi mahimmanci shi ne ka yi wa kanka da rayuwarka farin sani.


Matsalar mafi yawa daga cikin matasa ita ce ba su san kansu ba, don haka a kullum suke faɗawa cikin ruɗani da damuwa.


Dole ne ka gane wane ne kai, tare da manufofinka, ƙalubalenka da inda rayuwarka ta fuskanta.


Ka amsa waɗannan tambayoyin:


- Mene ne mafarkinka a rayuwa?


- A wasu ɓangarori kake da ƙarfi?


- A wasu ɓangarori kake da rauni?


- Wasu matsaloli kake da su?


- Wasu ƙalubalai kake fuskanta?


Ɗaya daga cikin sirrin mutane masu nasara shi ne sun fi sauran mutane fahimtar kawunansu, sun san abin da za su iya da wanda ba za su iya ba, da ƙalubalansu a rayuwa.


Ka tuna cewa in dai ba za ka iya amsa waɗannan tambayoyin ba, to duk abin da za ka karanta a shafuka na gaba ba zai amfane ka ba.


Sai an gano cuta ake iya maganinta.


2. Ka ayyana manufofinka.


Idan ka san kanka, to dole ka san abin da kake so a rayuwa.


Ina buƙatar ka ɗauki alƙalami da takarda ka rubuce dukkan wani abu da kake so ka samu ko zama a cikin wata 6 masu zuwa.


Idan ba za ka iya rubuta abin da kake so ba, to ba ka san abin da kake so ba.


Masana sun bayyana cewa rubuce manufa tana da matuƙar amfani wurin tattara hankalin mutum a wuri ɗaya tare da zaburar da shi don ƙoƙarin cika burinsa.


Shi yasa wasu suka bada shawarar ka rubuce manufofinka a takarda ko allo, sannan ka liƙe su a jikin bangon daƙinka ko wani wuri da za ka riƙa ganin su a kullum.


Mu ɗauka kai tela ne, manufarka sai ta zama ƙwarewa a kan sana'arka da kuma samun ƙarin kwastamomi nan da wata 6.


Ka koma lamba ta ɗaya ka duba matsalolin da ka rubuta, da su za ka gane manufofin da ya kamata ka ayyana don wata 6 na gaba.


Manufofinka za su iya zama:


1. Inganta alaƙarka da Ubangiji.


2. Ƙwarewa a kan baiwarka, misali rubutu, koyon kwamfuta, graphics design, content creation, da sauran su.


3. Neman ƙarin ilimi kamar haddan Alƙur'ani, karance wani adadi na littattafai, da sauran su.


4. Inganta zamantakewa da matarka ko mijinki.


5. Samun cikakken lafiya a jiki, da ruhi, da tunani, da sauransu.


3. Ka yi watsi da shagala


A wannan matakin, ina so ka lissafa duk wani abu da ke shagaltar da kai wanda ke hana ka cika wannan burin naka.


Shin Soyayya ce?


- Kana ko kina ɓata kuɗade wurin fira da saurayi ko budurwa a kullum.


- Ku ƙarar da awa 3 ko sama a rana tsakanin yin waya da chatting.


- Shiga damuwa saboda rigingimu na soyayya ko dan ba'a son ka/ki.


Shin wayarka ce?


- Kullum kana salwantar da rabin yini/wuni a kan waya ba tare da ka san abin da ka mora ba.


- Kai ne Facebook, Instagram, Tiktok, WhatsApp, kuma kowanne sai ka hau ka duba a kullum.


- Ka tambayi kanka, shin waɗannan kafafe akwai wata gudunmawar da suke bayar wa ga rayuwarka?


- Ta yaya za ka yi amfani da su domin kusantar burinka da ka lissafa a lamba ta biyu.


Shin miyagun abokai ne ko ƙawaye?


- Ko a makaranta, ko a gida, ko a kasuwa, ko a wani wurin, kana da abokai da kake tasirantuwa da su ta wata mummunar hanya?


- Shin suna ba ka shawara ne mara kyau ko kuma suna tunzura ka wurin aikata abin da babu amfani?


Ka zauna ka gano dukkan abin da ke hana ka dagewa da yin zuzzurfan aiki a kan burikanka.


Shagala ita ce halaka.


4. Ka canza wani abu da kake yi a kullum


To yanzu mun gama da ɓangaren fahimtar kai, da zayyano matsaloli da ƙalubalenka.


Idan ka iya kammala waɗancan matakan, daga na 1 zuwa na 3, to lokacin ɗaukar mataki ya yi.


Amma a nan ne, mutane da yawa suke gazawa.


Ai da ma magana ta fi komai sauƙi, aiki shi ke da wahala.


Idan ba za ka iya samar wa kanka da sauyin da rayuwarka take buƙata ba, za ka ci-gaba da rayuwa ne a cikin nadama.


DUBA WANNAN: Yadda Za Ku Sauya Rayuwar Ku A Rabin Shekara Kacal  (2)


Don haka ka shirya yaƙar dodanni da yawa idan kana son tsallake wannan matakin.


Amma waɗanne dodanni kenan?


Mu haɗu a fitowa ta biyu (2) da yardar Allah.


A karanta a yaɗa ga 'yan uwa.


Allah ya sa mu gudu tare mu tsira tare ɗan uwa.


Muna godiya da gudummawarku, Allah ya saka da alheri.


Da fatan za ku amfana da saƙonninmu a wannan shafin, ku ma ku gayyato abokanku don su ma su amfana.


Za mu ci-gaba Insha Allah.


Tushe/Asali: Hausa Motivation

Karanta Addu'ar Bayan Saukar Ruwan Sama

Karanta Addu'ar Bayan Saukar Ruwan Sama

مُطِرْنَا بِفَضْلِ اللهِ وَرَحْمَتِهِ.


Mutirna bifadlil-lahi warahmatih.



Addu'a Bayan Saukar Ruwan sama
Hoto: Sciencing

An yi mana ruwa saboda falalar Allah da Rahamarsa.

Wednesday 9 October 2024

Karanta Kammalallen Tarihin Rayuwar Annabi Sulaiman (A.S)

Karanta Kammalallen Tarihin Rayuwar Annabi Sulaiman (A.S)

Annabi Sulaiman (A.S) (Da Larabci: سُلَیمان ) ɗan Dawuda ne (A.S) kuma ɗaya daga cikin manyan annabawan Banu Isra'ila. Ya roƙi Allah Mulkin da ba wanda zai yi kamar sa a bayansa. Allah ya biya masa buƙatarsa ​​kuma baya ga mutane, ya sanya aljanu, aljanu, iska da tsuntsaye a ƙarƙashin ikonsa. An gina wajen ibadar Sulemanu a lokacinsa kuma bisa ga umarninsa.


Kammalallen Tarihin Rayuwar Annabi Sulaiman (A.S)
Hoto: Nurmuhammad

MarubuciSaliadeen Sicey


Sulaiman ɗan Dawud, Dawud shi ne Sarkin Isra'ila mai hikima kuma Annabin Allah (S.W.T). Sulaiman ya koyi ilimi mai zurfi a wurin mahaifinsa kuma ya kan shiga wajen mahaifinsa a lokacin sauraren ƙararrraki, Ya kasance mai kallo kuma ya koya daga wurinsa kuma a wasu lokuta yana ba da gudummawa A wajen zartar da hukunci.


Zuri'a


Sulaiman (A.S) ɗan Dauda ne (A.S) kuma ya fito ne daga zuriyar Yahuda ɗan Annabi Yakub (A.S). Annabi Sulaiman (A.S) yana da farar fuska da ƙaton jiki. An haife shi da kaciya.


Annabi Sulaiman (A.S) shi ne magajin mahaifinsa bayan wafatinsa yana da shekara ashirin da biyu ko goma sha uku.


Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bai wa Dãwũda da Sulaimãn ilmi, kuma suka ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah, Wanda Ya fĩfĩta mu a kan mãsu yawa daga bãyinSa mũminai."


Kuma Sulaiman ya gaji (ilimin) Dawuda. Ya ce: "Ya ku mutãne! An sanar da mu harshen tsuntsãye, kuma an bã mu dukan kõme. Lalle ne wannan, haƙĩƙa falala ce bayyananniya.


Kuma rundunarsa, daga aljannu da mutãne da tsuntsãye, aka tattara a wurin Sulaimãn, kuma aka jẽre su gabã ɗaya. (Karanta suratul An-namli 27:15-17).


Annabci da Mulki


Annabi Sulaiman (A.S) yana daga cikin manyan annabawan Banu Isra'ila kuma ya zama sarkinsu. 


Akwai ra'ayoyi da yawa game da zoben Sulemanu kamar yadda hadisi ya zo, Imam al-Mahdi (A.S) zai karɓa. Akwai kuma labarun camfe-camfe game da wannan zobe.


A zamanin Sulemanu (A.S), gungun mutane suna yin sihiri. Ya ba da umarnin a tattara dukan rubuce-rubucensu a ajiye a wuri na musamman. Bayan wafatin Suleman (A.S) sai wasu suka fitar da su suka fara koyarwa da wa'azin sihiri. Annabi Sulaiman (A.S) ya yi mulki tsawon shekaru arba'in. 


Iko da Mulki


Annabi Sulaiman (A.S) ya roƙi Allah da mulkin da babu wanda zai kama bayansa. Allah ya biya masa buƙatarsa ​​kuma ya sanya iska a ƙarƙashin ikonsa wadda ta yi nisa a cikin yini guda. Mutane da tsuntsaye da aljanu sun zama ƙarƙashin ikonsa. Yana ɗaure wasu aljanu marasa biyayya. Aljanu sun yi masa aiki kuma ya sami hanyar shiga ma'adinan zinariya.


Wajen Ibadar Sulemanu (A.S)


A bisa nassin Attaura, Allah ya yi wa Annabi Dauda (A.S) busharar gina wajen ibada mafi girma kuma mafi muhimmanci ga Yahudawa, “Gama sa’ad da kuka mutu aka binne ku tare da kakanninku, zan ta da ɗaya daga cikin zuriyarku. Zuriyarka, ni kuwa in sa mulkinsa ya yi ƙarfi, shi ne zai gina wajen ibada domin sunana, Zan kuwa tabbatar da gadon sarautarsa ​​har abada. Daga baya musulmi ne suka kira wannan wurin masallacin al-Aqsa (Kudus).


Halayen Maɗaukaki


Bayan mulki da iko mai girma, Allah ya bai wa Annabi Sulaiman (A.S) wasu gata;


Ayoyi da hadisai daban-daban sun ruwaito siffofi da yawa ga Annabi Sulaiman (A.S). Alkur'ani ya faɗe shi da bawan kirki mai yawan ambaton Allah kuma Allah ya ba shi ilimi. A cewar Kur’ani, Annabi Sulaiman (A.S) ya fahimci harshen dabbobi. 


A cewar wasu bayanin labarin Radd al-Shams ya faru ne ga Annabi Sulaiman (A.S). 


Littattafai na Misalai da Waƙoƙi an jingina su gare shi kuma duka biyun suna cikin littattafan Yahudawa masu tsarki.


Annabi Sulaiman (A.S) ya kuma yi hukunci. A cikin Alkur’ani an ambaci hukunce-hukuncensa. 


An ambaci sunan Sulaiman (A.S) sau goma sha bakwai a cikin Alkur'ani. Kur’ani ya ambaci labarai daban-daban game da Annabi Sulaiman (A.S), wanda ya fi shahara a cikinsu shi ne labarin Sarauniyar Sheba (Bilkisu Mai Gadon Zinare) Har ila yau, akwai labaru daban-daban game da shi a cikin hadisai, da yawa daga cikinsu masu bincike sun ce ba gaskiya ba ne da kuma ƙarin gishiri. 


Har ila yau, Kur'ani ya yi bayani ga kuskure na Sulaiman (A.S), bayan haka ya tuba. Allah kuma ya kira Sulaiman (A.S) 'Awwab' , wanda a zahiri yana nufin wanda ya sake komawa baya. Wannan yana nuni ne ga masu yawaita tuba zuwa ga Allah, kuma yana daga cikin mafi soyuwa a gare shi, wanda yake ba da lada mai yawa;


Kamar yadda Tafsir bn Kathir ya ce, a wata rana Sulaiman (A.S) yana kallon dawakan da suka ƙware sosai da nagartaccen kiwo, sai ya shagala da su, sai ya rasa lokacin sallar la'asar. Ya yi nadamar sha'awar kyawawan abubuwan duniya har ya manta da sallah ya rasa ambaton Allah. Sannan ya roƙi Allah gafara sannan kuma ya nemi yardar Allah.


Allah Ta’ala ya saukar da cewa: “ Kuma ga Dawuda Mun bai wa Sulaiman. Madalla da bãwa! Lalle shĩ, ya kasance mai yawan tũba."


Wata rana Suleman ya tara rundunarsa, ta bataliyoyin mutane, da aljanu, da tsuntsaye, da dabbobi daban-daban. Zai kai su ƙasar Askalon.


Suna wucewa ta cikin wani kwari, sai tururuwa ta ga rundunar da ke gabatowa, sai ta yi magana don ta gargaɗi sauran tururuwai: “Ku gudu zuwa gidajenku! Ga Annabi Sulaiman nan da rundunar sa. Annabi Suleman da jin wannan magana ta tururuwa sai ya yi murmushi. Ya yi murna da tururuwa ta san shi Annabi ne da ba zai cutar da halittun Allah da gangan ba. Ya godewa Allah da ya tseratar da rayukan tururuwai.


Allah Ta’ala ya ce: “ Kuma aka taru a gaban Sulaiman da rundunoninsa na aljannu da mutane da tsuntsaye, sai aka jera su gaba ɗaya. Har a lõkacin da suka je wa wani rami na tururuwa, wata tururuwa ta ce: "Yã kũ tururuwai! Ku gudu ku shiga rami ga Annabi Sulaiman nan da rundunar sa kada ya tattake ku."


Sai (Sulaimãnu) ya yi murmushi, yanã mai jin ni'ima da maganarta, kuma ya ce: "Ya Ubangiji! ayyuka na ƙwarai da za su faranta maka, kuma ka shigar da ni da rahamarKa a cikin bayinka salihai”. (Karanta suratul An-namli 27:17-19 Alƙur'ani).


A Urushalima, (Kudus) a kan wani ƙaton dutse, Sulemanu ya gina wajen ibada mai kyau don ya jawo mutane su bauta wa Allah. A yau ana kiran wannan ginin da sunan "The Dome of the Rock." Daga nan ne kuma wasu gungun mabiya da yawa suka bi sahun Sulaiman wajen gudanar da aikin hajji a Masallacin Harami na Makkah. 


Bayan sun kammala aikin hajji ne suka tafi ƙasar Yaman suka isa birnin San'a. Birnin ya burge Annabi Sulemanu ta ɓangaren dabarar su ta yadda suka bi da hanyar ruwa a dukan garuruwansu. Ya yi sha'awar gina irin wannan tsarin hanyar ruwan a ƙasarsa amma bai da isassun magudanan ruwa.


Sai Ya tashi ya ce a nemo Masa tsuntsun hoopoe (Al Hudahuda) wanda zai iya gano ruwa a ƙarƙashin ƙasa. Ya aika da sigina a ko'ina cikin jama'ar sa don a kira shi, amma ba a gan shi ba. A fusa ce ya bayyana cewa in dai tsuntsun ba shi da wani ƙwaƙƙwaran dalili na rashin zuwansa, zai hukunta shi hukunci mai tsanani.


Daga ƙarshe dai Al-Huda-huda ya zo wurin Annabi Suleman (A.S) ya na mai duƙar da kansa ƙasa cikin girmamawa, yana mai faɗin dalilin jinkirin sa ya ce "Na gano wani abu da ba ku sani ba, na je birnin Sheba (Sab'a) na dawo Muku da wani muhimman labari.


Annabi Sulemanu ya ce yana son ya sani, kuma ya huce fushinsa. Tsuntsun ya ci gaba da cewa: A “Sab’a Akwai wata katafariyar sarauniya mai suna Bilkis (Bilqis) da ke mulkinta, wadda ke da arziki mai yawan gaske, ciki har da wani ƙaton gadon zinare mai kyau, amma duk da wannan dukiya, Shaiɗan ya shiga zuciyarta da zukatan mutanenta. Ita ce take tafiyar da tunaninsu gaba ɗaya, na yi mamaki da na ga suna bautar rana ba Allah Ta’ala ba”.


Don Annabi Sulaiman Ya gaskata da wannan zance sai Sulemanu ya aiki Al Huda-huda da wasiƙa zuwa ga sarauniya Ya umurci tsuntsun da ya kasance a ɓoye kuma ya lura da komai.


Al Huda-huda yana tashi fir sai birnin Sab'a, sai fadar Bilkisu, yana shiga sai ya ajiye wasiƙar a gaban sarauniya ya tashi ya ɓuya. Cike da zumuɗi ta buɗe ta karanta: "Lalle daga Sulaiman yake, kuma haƙiƙa! Yana cewa: "Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai; muminai na gaskiya su ne waɗanda suka miƙa wuya.” (Ch 27: 30-31 Quran).


Sarauniyar ta shiga cikin damuwa sosai, ta yi sauri ta kira masu ba ta shawara. Don su mai da martani game da wannan ƙalubale, domin su ji cewa akwai wanda yake ƙalubalantarsu, kuma yana nuna musu zai yaƙe su sha kaye, Amma ya roƙe su, su yi biyayya ga sharaɗinsa.


Sai suka gaya mata cewa shawara kawai za su ba ta amma haƙƙinta ne ta ba da umarni a ɗauki mataki. Ta ce kuna so ku fuskanci barazanar mamayar Sulemanu da yaƙi? Don haka ta gaya musu: “Sulhu da abota sun fi kyau kuma sun fi hikima; yaƙi kawai ya kan jawo wulaƙanci, yana bautar da mutane, yana lalata nagarta. kyauta da sulhu kuwa za ta sa ta sami damar gano ko waye Sulaiman da jarumtakarsa, idan Annabi ne za ta fahimta idan kuma mai neman mulki ne za ta gane.


Shi kenan sarauniya Bilkis ta shirya mutanen ta da kayan dukiyoyi masu tarin yawa ta aika su zuwa wajen Annabi Sulaiman, domin su kai masa a matsayin gaisuwa domin ta jarraba cewa Annabi ne ko mai neman mulki da dukiya ne.


Tawagar Annabi Suleman sun je sun leƙo asirin labarin zuwan manzannin Bilkis da kyautar da aka aiko da ita kuma sun gaya wa Annabi Sulaiman, nan take ya ba da umarnin tara rundunar mayaƙa da tarin dukiyoyi kafin wakilan Bilkisu su kammala isowa. Da wakilan suka iso suka ga tarin runduna da dukiyoyi, sai suka gane cewa dukiyoyinsu ba komai ba ne kwatankwacin na daular fadar Suleman, wanda aka yi da itacen sandal da zinariya.


Sun lura Sulemanu ya leƙo asirin zuwansu sai suka yi mamakin yawan sojoji iri-iri, da suka gani, waɗanda suka haɗa da zakuna, damisa, da tsuntsaye. 


Sai manzannin suka tsaya cak a cikin mamaki, sun gane cewa suna gaban wata runduna ce da ba za ta iya tunkara ba.


Wakilan sun yi mamakin irin kayan ƙawan da ke kewaye da su. Suna ɗokin ba da kyauta da sarauniyarsu ta aiko su da ita kuma suka gaya wa Sulemanu cewa sarauniyar tana so ya karɓe su a matsayin sulhu. Abin da ya yi ya ba su mamaki: ko da yake bai nemi buɗe kyautar ba! Ya ce da su: "Allah ya ba ni dukiya mai yawa, da mulki mai girma, da Annabci. Don haka ni na wuce karɓar cin hanci, kawai burina shi ne in yaɗa imani da Tauhidi, da kaɗaita Allah."


Ya kuma umarce su da su mayar wa sarauniyar kyaututtukan kuma su gaya mata cewa idan ba ta daina irin ibadar da take yi ba zai tumɓuke mulkinta ya kori al’ummarta daga ƙasar.


Wakilan sarauniya sun dawo da kyaututtukan suka isar da saƙon. Sun kuma gaya mata abubuwan ban mamaki da suka gani. Maimakon ta yi fushi, ta yanke shawarar ziyartar Annabi Sulemanu da kanta. Sarauniya Bilkis ta bar Sheba tare da fādawanta da barorinta, ta aiki manzo ya faɗa wa Sulemanu tana kan hanyarta ya tarye/tarbe ta.


Annabi Suleman ya tambayi aljanu da ke masa aiki ko wani a cikinsu zai iya kawo masa gadon mulki kafin ta iso. Sai wani Aljani ɗaya daga cikinsu ya ce; "Zan kawo maka kafin a gama zaman nan."


Annabi Sulemanu bai mayar da martani ga wannan tayin nasa ba; ya bayyana cewa yana son akawo masa shi cikin sauri. Aljanu sun yi ta gwabzawa gasa da juna don faranta masa rai, wannan ya ce zai kawo nan da lokaci kaza, wannan ma ya faɗa. Can sai wani daga cikinsu mai suna Ifrit Ya miƙe tsaye ya ce: "Zan kawo muku shi a cikin ƙiftawar ido!"


Sai Ifrit Ya ce da Annabi Sulaiman ɗaga kanka sama sai ya ɗaga sai Ifrit ya ce sauke, Yana saukewa sai ga gadon Bilqis a gabansa Sulemanu lallai an kammala aikin kawo shi a cikin ƙiftawar ido. Kujerar Mulkin Annabi Suleman tana cikin Falasɗinu, ita kuma masarautar Bilqis ta kasance a Yemen, tafiyar mil dubu biyu. Wannan babbar mu'ujiza ce da ɗaya daga cikin waɗanda suke zaune tare da Annabi Sulemanu ya yi.


Lokacin da Bilqis ta isa fadar Annabi Sulaiman, an tarbe ta cikin fara'a da mutuntawa. 


Sai Sulemanu ya yi nuni ga gadon da aka ɗauko na Bilqis ya tambaye ta ko gadon ta da ta baro a Yaman ya yi kama da wannan? Ya kalleta, a ranta ta tabbata cewa lalle gadon nata ba za ta iya zama wadda take kallo ba, kasancewar nata yana cikin fadarta; da, ta gano kamanni mai ban mamaki kuma ta amsa: Sai tace "Kamar shi ne, kuma ya yi kama da nawa ta kowace fuska." Annabi Sulemanu ya tabbatar da cewa lallai Bilqis ta kasance mai hankali da iya diflomasiya.


Alkur'ani Ya ce:


TO A YAYIN DA TA ZO (FADAR ANNABI SULAIMAN ) SAI AKA TAMBAYE TA : KAMAR HAKA GADONKI YAKE? SAI TA CE ”YANA KAMA DA SHI”. TO ILIMIN DA AKA BA MU YA ƊARA HAKA, KUMA DUK MUN MIƘA WUYA GA ALLAH HAƘIƘANIN MIƘAWA”.


(Kur’ani sura ta 27 aya ta 42 ). 


Bayan ta gane cewa gadonta ne na mulki, sannan ta fahimci baiwar da Annabi Sulaiman ke da ita, sai ta shiga cikin ƙasaitacciyar fadar tasa. 


Daga nan ya gayyace ta zuwa cikin babban falo wanda aka shimfiɗa tiles da aka yi da gilas mai ƙyalli a zatonta ruwa ne, za ta shiga don haka ta ɗaga siket ɗinta sama saboda tsoron kar ta jiƙe kawai sai ta ji Annabi Sulaiman ya ce da ita: 


WANNAN AI FADA CE DA AKA GINA HANYOYIN TA DA GILASHIN KARAU “. 


(Kur’ani sura ta 27 aya ta 44) 


Alkur'ani ya ba mu labari cewa:


“ta dauka wani ruwa ne sai ta ɗage halliyarta [don ta ratsa ta]. Ya ce: "Lalle ne shi, gini ne mai santsi da gilashi." Ta ce: "Ubangijina! ( 27:44 ).


Ta yi mamaki, ba ta taɓa ganin irin waɗannan abubuwan ba. Bilqis ta fahimci cewa tana tare da wani mutum mai ilimi sosai wanda ba wai kawai mai mulkin babbar daula ba ne, shi ma manzon Allah ne. Ta tuba, ta bar bautar rana, ta yarda da imani da Allah, kuma ta nemi mutanenta su yi haka.


Bayan sun yi an gama ganawa: Bilƙis ta ga aƙidar mutanenta ta sauya a gaban Sulaiman. Sai ta gane cewa rana da mutanenta suke bautawa ba komai ba ce face ɗaya daga cikin halittun Allah.


A ranar hasken imani ya lulluɓe cikin zuciyarta da haskawa da hasken da ba ya gushewa, shi ne hasken Musulunci. 


Bilkis ta gane ashe masarautar Sulaiman ba kamar fadar da ta taɓa gani ba ce. Ta shaida hikimarsa da ƙasƙantar da kai tare da ƙarfin ikonsa kuma ta yarda da shi a matsayin manzon Allah. Ta tuba ta musulunta tare da al'ummarta.


Tarihin ziyarar sarauniya Bilkisu zuwa gurin Annabi Sulaiman, tarihi ne da ƙarshen sa ya zamo mai ban kaye sosai, inda a ƙarshe sarauniya Bilkisu ta ayyana da kanta cewa: 


” YA UBANGIJI NA LALLAI NA TAFKA KUSKURE (A BAYA) YANZU NA MIƘA WUYA GA ALLAH UBANGIJIN KOWA-DA-KOMAI, TA HANYAR ANNABI SULAIMAN”.


Kur’ani sura ta 27 aya ta 44.


A wata ruwayar an ce ta Aure Ta.


WAFATIN ANNABI SULAIMAN


Annabi Sulaiman ya rayu kuma ya yi mulki cikin ɗaukaka. Yawancin aikinsa na jama'a aljanu ne suka yi shi a matsayin hukunci don sanya mutane gaskata cewa aljanu ba su da ilimin gaibi. Sulaiman ya koya wa mutanensa cewa Allah ne kaɗai ya san irin wannan ilimin. Hatta wafatin Annabi Sulaiman ya zama darasi akan haka.


Aljanu ko annabawa ba su san makomar gaba ba, sai ga Allah shi kaɗai.


Sulaiman yana zaune riƙe da sandar sa, yayin da yake kula da wasu aljanu da ke aiki a cikin mahaƙar ma'adinai. Aljannun da suke tsoron Annabi sulaiman, sun mayar da hankali sosai kan ginin a lokacin da Allah ya yi niyyar ɗauke ran Annabi Sulaiman.


Ba wanda ya san mutuwarsa, sai bayan kwanaki, wata tururuwa mai yunwa ta fara lallasar/lasae sandarsa ta katako. Tana cikin ci sai sandar ta karye, gawar Annabi Sulaiman da ke jingine a kanta ta faɗi ƙasa. 


Mutane suka ruga wurin Annabinsu, nan da nan suka gane cewa ya rasu tun da daɗewa. Don haka kowa ya gane cewa da aljanu sun mallaki ilimin gaibi, da ba za su azabtar da kansu suna aiki tuƙuru ba, suna tunanin Sulaiman yana kallonsu. 


Rayuwa da mutuwar Sulaiman lallai suna cike da abubuwan al'ajabi waɗanda ɗan adam zai iya samun darussa masu ban mamaki daga gare su.


“Kuma a lokacin da muka wajabta wa Sulaiman mutuwa, babu abin da ya nuna wa aljani mutuwarsa face wata ƙwaro daga ƙasa tana cin sandarsa. To, a lõkacin da ya faɗi, ya bayyana ga aljannu cẽwa lalle ne dã sun san gaibi, dã ba su zauna a cikin azãba mai wulãƙantãwa ba. (Alkur'ani suratul Saba'i sura ta 34 aya ta 14 ).


Ya rasu a dhekara ta 931 kafin Haihuwar Annabi Isa (A.S) yana da shekaru 53 a duniya. 


MANAZARTA


Story of Prophet Sulaiman/Solomon (Pbuh) Na Ibn Kathir.


Don neman ƙarin bayani ku tuntuɓi IslamAwareness@gmail.com domin faɗaɗa bayani ko bincike.

Monday 7 October 2024

Karanta Gajerun Sakonnin Yabon Sassan Jikin Masoyiya

Karanta Gajerun Sakonnin Yabon Sassan Jikin Masoyiya

Idanuwanta tamkar an sato taurari guda biyu a sama an sanya mata su.


Saƙonnin Yabon Sassan Jikin Masoyiya
Hoto: Photo done

Marubuci:- Prince E


Hancin ta a tsaye yake kamar eriyar/ƙeriyar rediyo.


Laɓɓan bakinta masu taushi kamar furen turaren zubardaj.


Lafuzzan bakinta da halayenta masu tashi kamar gajimare.


Yatsun hannuwanta kamar tsintsiya, dogaye sirara kamar an feƙe da shafana/shafino.


Ga ta da murmushi mai jan hankali mai shiga jiki har zuciyar mai kallon ta, tamkar sanyin safiyar asubahi.


Tafiyar ta cikin lumana babu baragada/sauri kamar mai tausayin ƙasa.


Ga ta kyakkyawa irin wacce kowanne saurayi ke mafarkin mallaka.


Allh Sarki ƙanwata, har yau ba a ƙirƙiri haruffan da za su iya bayyana ainihin kyawunki a rubuce ba.


Matsayinta a cikin mata tamkar zinariya ce a cikin ɓaƙaƙen ƙarfe da dangoginsa.


Ke ce na nuna ƙanwata.


Ina ma hannayena za su iya taimaka mini na tashi sama, da na yi amfani da su na keta giza-gizai na taho wurinki.


Kina raina ƙanwata, ƙaunar da nake miki ta fi wacce makaho yake yi wa idanuwa.


Zuciyata idan tana tunaninki tamkar ta tsago ƙirjina ta taho nemanki da kanta.

Zan Bar Muku Najeriyarku Na Koma Kasata - Fati Niger

Zan Bar Muku Najeriyarku Na Koma Kasata - Fati Niger

Fati Niger ɗaya ce daga cikin fitattun mawaƙan Kannywood, a ɗaya daga cikin sababbin waƙoƙin ta da ta saki na baya, bayan nan, tana mai nuni da yadda take fama da ƙalubale a zaman ta a Najeriya.


Zan Bar Najeriya Na Koma Ƙasata - Fati Niger

A saboda haka ne take tunatar da masoyan ta da maƙiyanta a fakaice cewa tana da ƙasa, za kuma ta je can amma za ta dawo.


Waƙar mai taken "Fati Fatima Fatiti.".


Ga kaɗan daga cikin wasu baitocin da ke bayyana irin halin da take ciki;


Ba ku zamtowa daidai da ni.


Maƙiyana dole ku bar mini.


Lokacin Allah ke yi da ni.


Ciwuka ba sa rasa magani.


Na riga ni nai nisa tuni, don ko sunana ya kai gurin da ni ma ban je ba.


Sanannen mawaƙin nan na Kannywood Ado Gwanja shi ne ya yi mata amshin waƙar, amshin da ke nuni da yadda yake lallashin ta kan yanayin da ta kasance a ciki.

Sunday 6 October 2024

Karanta Addu'a Yayin Da Ruwan Sama Yake Sauka

Karanta Addu'a Yayin Da Ruwan Sama Yake Sauka


اللّهُمَّ صَيِّـباً نافِـعاً .


Allahumma sayyiban nafi'an.


Addu'a Yayin Da Ruwan Sama Yake Sauka
Hoto: Schultz Soft Water

Ya Allah! Ka sanya shi ya zama ruwa (mamako), mai amfani.


Saturday 5 October 2024

Zafafan Darussa 10 Da Ba Za Ku Same Su A Makarantu Ba

Zafafan Darussa 10 Da Ba Za Ku Same Su A Makarantu Ba

Darussan rayuwa 10 waɗanda ba za a koyar da kai a makaranta ba, amma rayuwa za ta sanar da kai.


Darussan rayuwa
Hoto: Orfonline


1. Rayuwa ba gasa ba ce.


Kowa ka gani a rayuwa yana da nasa tafarkin da ƙaddarar wacce ta sha bamban da na sauran mutane. Don haka ka bar haɗa kanka da wani, kowa a rayuwa yana da rabonsa.


2. Lafiyarka ta fi komai muhimmanci.


Ba za a karantar da kai wannan a makaranta ba, amma rayuwa za ta karantar da kai da zafi. Ba ka da wata kadara ko mallaki da ya wuce lafiyarka.


Idan rashin lafiya ya kama ka, duk wani abu da kake yi a baya ba za ka iya yin sa ba, don haka ka kula da lafiyarka yadda ya kamata domin lafiyar mutum ita ce jarinsa.


3. Farin ciki daga zuciya yake


Yawan dukiya, shahara da ɗaukaka, ko jin daɗi duka ba su ke samar da farin ciki ba. Idan kana da wadatar zuci za ka samu farin ciki da kwanciyar hankali wani kuwa duk abin da yake so a rayuwa yana da shi amma duk da haka cikin damuwa yake kwana.


4. Ba kowanne zance a ke tankawa ba.


Idan ka ce za ka tsaya ka jefi duk wani kare da yake haushi a kan hanyarka ba za ka taɓa isa inda kake so ka je ba. Don haka, ba duk abin da aka faɗa ko aka aikata maka za ka tankawa ba.


Wani lokacin shiru shi ne abu mafi dacewa ga wanda yake neman ka da rigima ko faɗa.


5. Ba za ka iya burge kowa ba a rayuwa.


Duk abin da za ka yi wa mutane, sai wasu sun ji haushinka ko sun tsane ka. Ka yi iya ƙoƙarinka don ka zauna da mutane lafiya, amma ka sani duk abin da za ka yi, ba za ka iya burge kowa ba.


Don haka kada ka yi mamaki don wani ya tsane ka ba tare da dalili ba, saboda wasu mutanen a haka ɗabi'arsu take.


6. Lokaci ya fi komai tsada a rayuwa.


Komai yana da lokaci a rayuwa, don haka ka yi komai a lokacinsa. Duk abin da ya kucce/kuɓce maka za ka iya dawo da shi amma banda lokaci. Idan lokaci ya wuce ya wuce kenan har abada. 


7. Abokai na gaskiya suna da wuyar samu.


Mutane da yawa sukan gina abokantaka ne akan amfanuwa ko saboda abin duniya.


Idan Allah Ya azurta ka da aboki ko Ya azurta ki da ƙawa mai kyawun hali kuma wanda yake son ka da alheri, ka riƙe sa da kyau. Abokai na gaskiya suna da wahalar samu.


8. Tafiya ta fi mahimmanci bisa ga masauki.


Idan ka cika damuwa da sakamakon da kake nema, za ka iya rasa darussa masu muhimmanci da akan koya a cikin hanya.


Kafin isa ga masauki ko burin da kake nema, akwai doguwar tafiya wacce take ɗauke da tarin darussa kuma muhimmancinta daidai yake da na wannan burin da kake nema.


9. Gazawa ɓangare ne na nasara.


Duk wani mutumin da ya yi nasara ya taɓa faɗuwa a wani mataki na rayuwarsa. 


Faɗuwa dama ce da take ƙarfafa azamarka da juriyarka kuma ta karantar da kai abubuwa masu yawa da ba za ka sani ba idan da nasara ta zo gare ka kaitsaye.


10. Tunaninka shi ne kamanninka.


Abin da ka yarda da shi game da kanka da kuma duniyar da ke kewaye da kai su ke hukunta zahirin rayuwarka. Don haka domin canza rayuwarka, dole sai ka fara canza tunaninka.


Waɗannan darussa ne masu muhimmanci amma masu hankali kaɗai kan gane.


Allah Ya ganar da mu!


Tushe/Asali: Hausa Motivation

Friday 4 October 2024

Karanta Gajerun Kalaman Soyayya Masu Dadi

Karanta Gajerun Kalaman Soyayya Masu Dadi

Na yi mamakin ganin yadda nake shirin afkawa dajin da ke cike da sarƙaƙiya, dajin da kowa ke tsoronsa, sai dai hankalina ya kwanta ne tun daga lokacin da na gano cewa kina da nutsuwa da girmama mutane, na san za ki kawo guzuri ga mai shirin tunkarar bakin daji mai nisan tafiyar da ba a san iyakarta ba, mai cike da bishiyar farin ciki da ta ƙunci, nishaɗi da ɓacin rai, samun amincewar ki shi ne kaɗai burina.


Gajerun Kalaman Soyayya Masu Daɗi
Hoto: Adobe Stock

Marubuci:- Prince E


Na damu da ke ya kamata ki sani, ni fa zancen ki nake so, lafazin harshenki abin a so ne, 'yan maza na son ki da wawaso, kin ce musu ni za ki so.


Kyakkyawar gimbiya kin sacen zuciya, kin iya soyayya.


To mene ne sirrin? Shin hasken ƙwayar idanunuwan ki ne, ko kyautatawarki gare ni ce? Kallo ɗaya tak na yi miki nan take sai na ji tamkar na dawwama ga kallon kyakkyawar fuskar da na gani, wacce ta haɗo dukkan wasu shikashikai na kyau.


Sannunki sarauniya mai kyawun duniya, kin iya soyayya kamar a ƙasar India.


Haƙiƙa sabo wawan abu ne, bai yi shawara da ni ba lokaci guda na ji na saba da ke tamkar wacce na ɗauki tsawon shekaru muna tare.


Na gaishe ki sarauniyata mai mulkin birnin alƙaryar zinariyar zuciyata.

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (3)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (3)

A tsammanin ta bai isa ya zo wurin ba a wannan lokacin, domin su a abin hawa suke, shi kuwa a ƙasa yake. Tana zuwa ta same shi ya haɗa kai da gwiwa yana ta kiran sunanta, "Laila! Ya Laila!! Ya Laila!!!" Ta ƙaraso wurinsa tana mai cewa, "Ya Majnunun Soyayya ga Lailarka ta iso!!". Duwatsun kusa da na nesa suka ɗauki muryarta tana amo.


Labarin Soyayyar Majnun Da Laila
Hoto: Dynamite of emotions

Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Nan da nan ya zabura zuwa gare ta, yana mai cewa, "Shin da gaske ne Laila ke ce anan?" Ta amsa "Ni ce!" Ya miƙa mata hannu ta riƙe sai suka ji kururuwar mahaifanta suna nemanta domin a ci-gaba da tafiya. Ta juya da hanzari, ya ce, "Haba Laila kada ki tafi ki bar ni da begenki!" Ta ce, "Kar ka damu, idan na dawo za mu haɗu anan."


"Yaushe za ki dawo?" Ya tambaye ta. Ta ce, "Ban san lokacin ba, amma da zarar mun taho zan aika maka." Da haka ta tafi ta bar shi anan. Majnun ya ce a ransa, "idan ta dawo wa za ta aika ya faɗa min? A ina ɗan saƙon zai same ni? Kawai bari na zauna anan ɗin har sai ta dawo." Ya share wuri ya zauna ba shi da wani abinci sai ganyen bishiyar da ke wajen yana shan ruwan da ke ɓuɓɓugowa daga ƙarƙashin dutse. A kullum zancensa shi ne kiran sunan Laila da addu'ar ta dawo ta same shi. A haka har tsiron bishiya ya fito daga 'ya'yan itacen da yake jefarwa, ganyenta ya nannaɗe masa jiki ya zama tamkar bishiyar a jikinsa ta tsiro.


A can garin da su iyayen Laila suka je da ita kuwa, sai wani attajiri ya fito yana son ta da aure. Nan take ya ba wa iyayen raƙuma ɗari gami da wasu kyautuka masu yawa. Da Laila ta ga alamar lallai za a aurar da ita gare shi sai ciwo ya kama ta. Ta yi ta fama, iyayen suka yi nufin komawa gida domin magani alabarshi idan ta warware sai a yi auren. A hanyar su ta dawowa suka sauka a wannan zangon. Duk da tana fama da jinya Laila ta taso zuwa wurin da suka yi alƙawari da Majnun. Ta kusa isa kenan ta gamu da wani mutum ya ce mata, "Yarinya kada ki je wurin nan da kika nufa. Akwai wata fatalwa mai kamar bishiya da ta bayyana."


Kullum tana kiran sunan "Laila, Laila." Da ta ji haka sai ta tabbatar Majnun ne bai tafi ba. Ta ƙarasa wurin da gudu. Yana ganinta ya yi zumbur ya miƙe tsaye yana mai farin ciki, yana cewa "Laila kin cika alƙawari? Laila ke ce kuwa? Laila za ki aure ni??" 


Kasancewar ya jima sosai a zaune ba ya miƙewa, sai jiri ya ɗebe shi, a lokaci guda kuma zuciyarsa ta buga saboda tsanannin farin ciki. Kansa ya gwaru da dutse ya faɗi sumamme.


Laila na ganin irin wannan sadaukantarwa ta kasa haƙurcewa, zuciyarta ta raurawa, ƙirjinta ya yi matuƙar ƙunci. Nan take numfashinta ya ɗauke ta faɗi a wajen sumammiya ita ma.


Kays Majnun shi ne ya fara farfaɗowa daga sumar da suka yi gabaɗayansu, ya yunƙura da zummar isa inda Lailan take amma sai ya kasa yunƙurawar saboda ba kuzari a tare da shi, cikin wata murya ma'abociyar raurawa ya ƙwalawa Laila kira "Laila...!" shirun da ya biyo baya shi ne ya tilasta masa fara jan jiki a kwancen, a hankali yana jan jiki har ya ƙarasa inda Lailar take a kwance a sume.


Cikin ruɗewa da firgici Majnun ya ringa kiran sunan Laila ganin ba ta ko alamar motsi, ya ce "Kada ki tafi ki bar Majnuninki a cikin azabtacciyar rayuwar da gwara mutuwa da ita, kin sani cewa Majnun da son ki yake rayuwa Laila..." ya ƙarashe kalaman nasa da wasu daɗaɗan baitoci:


Rabuwa da ke ba daɗi na ji a jikina.


Kar ki bar ni Lailata domin kuwa ke ce jin daɗina...'


Farin ciki ne mara misaltuwa ya bayyana ƙarara a fuskar Majnun dai-dai lokacin da ya ga Laila ta motsa.


A dai-dai lokacin da Lailar ta motsa har ma ta samu ta zauna, kuma a lokacin ne iyayen Lailar suka ƙaraso wajen da suke, iyayen Lailar suka ruɗe ganin yadda suka ga 'yarsu a wani mawuyacin hali.


Suka ɗauki 'yarsu da zummar tafiya da ita wani garin daban wanda yake da nisa daga wannan nahiyar, ''Laila..." Majnun ya ƙwala mata kira da ƙarfi ganin har sun fara yin nisa daga wajen da suka bar shi a kwancen, ƙwala mata kiran da ya yi shi ne ya yi sanadiyar ƙara dakusar da ɗan ragowar kuzarin da ke tare da shi, don haka yana gama ƙwala mata kiran sai ya kuma kifewa a ƙasa sumamme.


DUBA WANNANAsalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (4)


Laila tana ganin hakan sai ta ruɗe, ta kufce daga hannun iyayenta ta rugo izuwa gare shi.


Za mu ci-gaba Insha Allah.

Wednesday 2 October 2024

Dariya Dole: Ma'aurata Da Aljanu

Dariya Dole: Ma'aurata Da Aljanu

Wani Ango ne ya yi sabon aure shi da matarsa suka tare a sabon gida, kullum kafin su kwanta bacci sai ta wanke kwanukan da aka ci abinci, da tukwane gaba-ɗaya, amma idan safiya ta yi gari ya waye sai su ga duk an ɓata kayan da ta wanke, sai su yi ta mamaki ya haka? Me yake faruwa ne?


Ma'aurata Da Aljanu
Hoto: Maple knoll

Sai suka yanke shawarar cewa yau ba za su yi bacci ba sai sun ga mai yin wannan aikin, dare ya yi dare, sai suka ji an fara motsi a cikin gida, sai suka leƙo su ga ko su wane ne, suna leƙowa kuwa sai suka ga wasu irin halittu sun ɗora girki a kan tukunya, cikin minti biyu abinci ya dahu.


Sai aka fara rabo kamar haka;


Ɗauki wannan ka kai wa Ifritu yana ƙasar India.


Kai kuma miƙa wa Turwas yana ƙasar China.


Kai kuma yi sauri ka je ƙasar Masar (Egypt) ka kai wa Sharfayailu.


Karɓi wannan ka miƙa wa ango da amarya na cikin gidan nan, tun da yau sun laɓe suna kallon mu.


Tushe/Asali: Babu hanyar tabbatar da ainihin mamallakin rubutun, saboda rubutun yana yawo ne ba tare da asalin sunan mamallakin shi ba.

Tuesday 1 October 2024

Karanta Ainihin Tarihin Rayuwar Ibn Taimiyya

Karanta Ainihin Tarihin Rayuwar Ibn Taimiyya

Cikakken sunan Ibn Taimiyyah shi ne ' Taqiy al-Din 'Abu al-Abbas 'Ahmad ibn 'Abd al-Hallim ibn 'Abd as-Salam ibn ' Abdullah ibn al-Khiḍr ibn Muḥammad ibn al-Khiyr ibāllīr- ibn al-Khiḥr Ḥarrānī : أحمد بن عبد الحليم بن عبد السلام بن عبد الله بن الخضر بن محمد بن الخضر بن إبراهيم ب اللهن علي بن علي بن بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن عبد السلام .


Ainihin Tarihin Rayuwar Ibn Taimiyya
Hoto: Asharis assemble


MarubuciSaliadeen Sicey


Sunan Ibn Taimiyyah ( ابن تيمية ) ba a saba ganinsa ba ya samo asali ne daga wata mace daga cikin iyalansa saɓanin namiji, wanda al'ada ce ta da a lokacin kuma har yanzu. Laƙabin " Taimiyya " ya fito ne daga kakarsa wacce ake kira Taimiyyah. Ta kasance mai nasiha kuma an yi masa laƙabi da " Ibn Taimiyyah ". Taimiyya ta kasance fitacciyar mace, shahararriyar mai ilimi da taƙawa da sunan Ibn Taimiyya da yawa daga zuriyarta maza ne suka karɓa.


Ibn Taimiyyah, sunan haihuwa Taqī ad-Dīn ʾAḥmad ibn 'Abd al-Hallim ibn 'Abd al-Salam al-Numayrī al-Harrani, malamin Sunna ne, muhaddith, alkali, Salafist kuma masanin siyasa.


Ahmad ɗan Abdulhalimu ɗan Abdussalami ɗan Abdullahi ɗan Haliru ɗan Muhammadu ɗan Haliru ɗan Aliyu ɗan Abdullahi. Ya shahara da sunan Ibnu Taimiyyah saboda kakarsa da ake kira Taimiyyah. Ana kuma ce ma sa “Majduddini”. Sannan ana ce ma sa “Numairi” saboda shi dan kabilar Banu Numairi ne.


Sannan ana ce ma sa kuma “Harrani” saboda Harrana ne garin da aka haife shi. ( Yanzu Garin Yana Cikin Kasar Turkey 🇹🇷).  


Sannan ana ce ma sa “Dimashki” saboda a garin Dimashka ( Damascus Syria 🇸🇾 ) ne ya girma, ya yi karatu. 


ASALINSA


Ibnu Taimiyyah ɗan asalin ƙasar Turkiyya ne. Don an haife shi a garin Harrana wadda take arewa maso gabashin ƙasar ta Turkiyyah.


Haihuwa


An haife shi ne a ranar litinin 10 ga watan Rabi’ul Awwal 661H Wanda Ya zo dai-dai da 22 Janairu 1263, Amma bayan shekaru shida sai iyayensa suka yi hijira daga ƙasar zuwa ƙasar Siriya inda suka sauka a babban birnin Dimashka, hedikwatar Sham.


Dalilin hijirar tasu kuwa shi ne kaucema fitinar ‘yan Tattar waɗanda suka auka ma garuruwan musulmi suka yawaita ɓarna da zubar da jinin bayin Allah. Game da mahaifansa kuwa, shi ɗan gidan malamai ne domin ya sami kansa a tsakanin iyaye da kakanni da ‘yan’uwa ma’abota karatu. A lokacin da za su yi hijira kuwa babu abin da ya wahalar da su kamar littafai da ke tare da su masu ɗimbin yawa, ga shi kuma suna gudun maƙiya.


Al-harran garin da aka Haifi Shaihil Islam Ibn Taimiyya
Hoto: Wikipedia

Ba domin kiyayewar Allah ba ma ba za su tsira da rayukansu zuwa Sham ( Syria 🇸🇾) ba. Isarsu ƙasar Sham ke da wuya mahaifin Ibnu Taimiyyah Shihabuddini ya fara koyarwa da wa’azi a babban masallacin Jum’ah na Dimashka wanda ake kira Al-Jami’ul A’azam masallaci mafi girma. 


Daman shi fitaccen malamin furu’a ne a mazahabar Hambaliyya. Nan take aka shugabantar da shi ga babbar makarantar hadisinnan da aka sani Darul Hadis As-Sukkariyyah, aka kuma ba shi gida a cikin makarantar in da nan ne Ɗansa Ibnu Taimiyyah ya girma. Kafin haka, kakan Ibnu Taimiyyah Majduddini sanannen malami ne da ya yi wallafe-wallafe a fannin hadisi da Usulul Fiqhi  shi ne mawallafin littafin nan na Muntakal Akhbar wanda Imamus Shaukani ya yi wa sharhi a cikin Naulul Audar. Haka ma baffansa Fakhruddini, malami ne fitacce da ya wallafa babban littafin Tafsirin Alqur’ani. 


Shi ne kuma wanda ya gaji Ibnul Jauzi a kujerarsa ta karantarwa da babban mumbarinsa na Bagadaza.


Kuma IbnuTaimiyyah ya yi karatu a wurinsa.


Mahaifa


Harran gunduma ce a gundumar lardin Şanlıurfa a ƙasar Turkiyya. Yanki ne mai faɗin kilomita 96 kuma yana da yawan mazauna 96,072 a lissafin shekarar (2022). Garin Ya na da kusan kilomita 40 (mil 25) kudu maso gabas da Urfa da kilomita 20 (mil 12) daga mashigar kan iyakar Siriya ta Akçakale.


Mahaifar Ibn Taimiyya
Hoto: Onedio

An kafa birnin Harran a wani lokaci tsakanin ƙarni na 25 zuwa 20 kafin haihuwar Annabi isa (AS) (BC), mai yiwuwa ya kafu a matsayin birnin 'yn kasuwa na Sumerian. A tsawon tarihin farko birnin Harran ya girma cikin sauri zuwa babbar cibiyar al'adu, kasuwanci da addini ta Mesopotamiya. Kuma ya sha zama babban birnin lardi sau da yawa a matsayi na biyu mafi muhimmanci ga babban birnin Assuriyawa na Assur da kanta. A lokacin rugujewar Daular Assuriya, Harran ya ɗan yi aiki a matsayin babban birnin ƙarshe na Daular Neo-Assyrian (612-609 BC).


Harran
Hoto: Holy land photos

Daular Mongol ta mamaye birnin a shekara ta 1260 kuma ta lalata kusan dukkan birnin, mutane sun bar garin har shekara zuwa ta 1271. Duk da cewa an bar Harran a matsayin sansanin soja a ƙarƙashin wasu gwamnatoci a baya, amma a cikin ƙarni na biyar da suka wuce an yi amfani da shi azaman wurin zama na wucin gadi ta wurin makiyaya na gida. Al'ummomi Harran sun koma cikin ƙauye na dindindin a cikin shekarun 1840s, amma kwanan nan Harran ya girma zuwa birni na dindindin ta hanyar ci gaban ban ruwa na aikin gona na cikin gida. Harran gundumar Turkawa ce har zuwa 1946, bayan da aka mayar da ita zuwa wani yanki na gundumar Akçakale. Ta dawo da matsayinta na gunduma a cikin shekarar 1987.


Birnin Harran
Hoto: Pinterest

A yau, babban wurin yawon buɗe ido ne na cikin gida. Garin ya shahara musamman da kiwon ƙudan zuma waɗanda ke da alaƙa da gine-ginen da suka riga suka kasance a Harran a zamanin Mesopotamiya ta dā.


Tashinsa da Iliminsa 


Ibnu Taimiyyah ya tashi a gidan ilimi kamar yadda muka gani. Ya kammala hardar Alƙur’ani tun a lokacin ƙuruciya. Sannan ya kula da sanin ilimomin Fiƙihu da Hadisi da Tafsiri da Arabiyyah.


 Tarihin Ibn Taimiyya
Hoto: Usman Abdullah Malik

Ya soma karantarwa da fatawa da rubuta littafai da tattaunawa da malamai Munazara tun bai wuce shekaru 20 Ba. Koda ya cika shekaru 30 an fara yi masa laƙabin Mujtahidi kuma “Mairaya Sunnah”. Yana da matuƙar wuya a iya siffanta baiwar da Allah ya yi wa Ibnu Taimiyyah ta fuskar ilimi. Masu ba da labarinsa na ganin kasawarsu wajen bayyana irin hikimomin da ke tattare da shi ta wannan haujin. An lisafta malaman da ya gurfana a gabansu don ɗaukar karatu aka tarar sun zarce malamai 200.


Akwai kuma littafan da ya karanta su sau da yawa a wurare daban-daban kamar Musnad na Imamu Ahmad. 


Game da nasa littafai shi kuma, Ibnu Taimiyyah ya wallafa sama da littafai hamsin a fannona daban-daban na addini, banda jananan wallafe-wallafensa da aka tara cikin Majmu’ul Fatawa mai sifili talatin da bakwai. 


Ya ishi mai karatu misali abin al’ajabi cewa, duk da yake Ibnu Taimiyyah bai wallafa Tafsirin Alƙur’ani ba, amma malamai daga bisani sun wallafa shi daga cikin littafansa. Ma’ana an tattara wuraren da ya yi sharhi akan ayoyin Alƙur’ani daga ciki littafansa a tsakankanin maganganunsa da kafa hujjojinsa, sai ga shi an samu kusan kammalallen Tafsiri mai Mujalladi huɗu. 


Mujaddadi Ibnu Taimiyyah muna iya cewa, Allah gwanin sarki ya tashi Ibnu Taimiyyah ne a wani lokaci da buƙatar irinsa ta yawaita. Don kuwa a wancan lokaci al’umma tana fama da matsaloli da rikici da tashin hankula na ciki da na waje. Daga cikin gida musulmi na fama da rabuwar kai, da yawaitar ƙungiyoyi da yaɗuwar bidi’ah da raunin ilimin furu’a.


Ga kuma lalacin da ya zo a cikin jama’a da zaluncin sarakuna da kwaɗayin malamai. Tsibbace-tsibbace da bokanci da duba sun zama gama-gari a cikin al’umma. Daga waje kuma ‘yan mishan sun kai ma musulmi farmaki, ‘yan Shi’ah masu kiran kansu Fadimawa sun haɗa kai da su. Sannan ga Tattar sun shelanta mummunan yaƙi da musulunci da musulmi a duk in da suke a wancan lokaci. 


Shaihun musulunci ya fuskanci duka waɗannan matsaloli da nufin magance su. Ya kuma samu taimakon Allah matuƙa a wajen cimma wannan burin nasa.


Mutum ne da aka suffanta shi da kaifin basira da ƙarfin ƙwaƙwalwa, har wasu ma na ganin bai taɓa sanin abu ya manta da shi ba. Yana da ƙarfin tuna ayoyin Alkur’ani da nassoshin hadissai da maganganun malamai na kowane fanni. Don haka ya kasance mai kaifin hujja wadda take yanke wuyan abokin gaba nan take.


Ga shi kuma jarumi da ba ya tsoron ko-ta-kwana. Don haka ba ya da ja da baya ga abin da ya sa gaba. Sannan yana da kwarjini a idon jama’a da kyawawan ɗabi’u da suka daɗa soyar da shi ga mutane. Ga shi mutum mai kishin gaskiya da ƙoƙarin yaɗa ta. Haɗa da halinsa na gudun duniya da rashin kula da jin daɗinta. Irin wannan malami Allah ya ɗora shi a kan kyakkyawar hanya irin ta Annabawa wane irin canji kake tsammanin al’umma ba za ta ci moriyarsa ba ta hanyarsa? 


Ɗan Taimiyyah nan take ya rurrusa aƙidun da suka zame ma musulunci tsutsar goro ta hanyar rubuce-rubucensa da wa’azozinsa da karantarwarsa. Ya kece raini a wajen wargaza aƙidun Yahudawa da na ‘Yan mishan. Ya yi faɗa da ƙungiyoyi mabiyan son zuciya irin mulhidai da zindiƙai da ‘yan Shi’ah da waɗanda suka wuce wuri a Sufanci.


Ya yi kira ga koma ma littafin Allah da Sunnar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba tare da ta’assubanci ga wani mutum ko ƙungiya ko mazhaba ba. 


Sa’annan ya kira sarakuna da talakawa zuwa ga yaƙar kafirai waɗanda suka keta hurumin musulmi, musamman dai Tattar. Ya kuma fita ya yi yaƙi a matsayin ɗaya daga cikin sojoji. Tare da haka kuma Ibnu Taimiyyah ya kafa wata makaranta da Allah ya yawaita almajiranta tun daga wancan zamani har zuwa yau, kuma tana ci gaba da bunƙasa har a naɗe ƙasa.


Wannan makaranta tasa tana mutunta magabatan Sahabbai da Tabi’ai da waɗanda suka biyo bayansu, da shugabannin mazhabobi, tana kuma la’akari da ra’ayoyinsu da fatawoyinsu baki ɗaya. Tana kuma rinjayar da nassi ingantacce idan ya zo daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a kan maganar kowa kome darajarsa. 


Wannan makaranta dai tana da ɗaruruwan littafai da dubban malamai a cikinta. Dukkaninsu suna jingina kansu ga Sunnah da bin magabata ba ga shi Ibnu Taimiyyah ɗin ba. Jarabawar da Ibnu Taimiyyah ya gamu da ita yana da wuya Allah ya ɗaukaka wani bawansa ba tare da ya gamu da wata jaraba ba a rayuwarsa. Wannan ita ce sunnar Allah ga Annabawa da malamai mutanen kirki.


Shehun musulunci ya gamu da jarabce-jarabce da dama a sakamakon jihadinsa na makami da na alƙalami waɗanda suka dagula ma sa jin daɗin rayuwa. 


Zan faɗi wasu daga cikinsu a takaice kamar yadda suka zo a tarihinsa daga littattafai da dama.


A shekarar 696H ya gamu da ƙyashi daga abokan tafiya, malamai, waɗanda suka ɗauki littafinsa Al-Fatwal Hamawiyyah suka kai ƙararsa da shi a wurin mahukunta. Sun bi duk hanyoyin da suke iyawa wajen murza maganarsa da ba ta irin ma’anar da suke so su jingina ma sa. A wannan lokaci sarki Saifuddin Jagan ya goyi bayan Ibnu Taimiyyah, ya kuma husata da waɗanda suka kafa adawa da shi. Don haka wannan jarrabawa ba ta daɗe ba ta gushe.


A shekarar 705H lokacin da farin jinin Ibnu Taimiyyah ya gama bayyana, bayan an ga rawar da ya taka a yaƙin da aka yi da Tattar, har kuma ya samu kusanci da hukuma abin da ya ba shi damar sa a kawar da wasu ɓarnace-ɓarnace. Nan take sai ƙurjin hassada ya sake tashi a zukatan wasu malamai daga cikin sufaye.


Sai wani malami da ake kira Nasrul Mambiji da wani malami bamalike ana ce ma sa Ibnu Makhluf suka tafi hedikwatar masarauta da ke ƙasar Masar ( Egypt 🇪🇬 ) su ka kai ƙarar Ibnu Taimiyyah suna tuhumar sa da gurɓata aƙidun jama’a.


Suka kafa hujja da littafinsa na Al-Akidatul Wasiziyyah. A nan ma sarki ya ba da umurni aka zaunar da shi tare da manyan malamai in da aka karance littafin nasa, daga ƙarshe kuma aka barrantar da shi daga saɓa ma magabata.


Sai ma a wannan karon ya samu takardar yabo daga Sarkin Musulmi. Wata ɗaya bayan faruwar wannan, sai waɗannan malaman suka sa sarki ya rubuta ma sa wata takarda ana neman sa da zuwa Misra ( Egypt 🇪🇬) don ya bayyana a gaban sarki. A wannan karon da tuhumar yana neman sarauta! 


An dai zaunar da shi a gaban Ibnu Makhluf don ya yanke ma sa hukunci, abin da ɗan Taimiyyan ya ƙi yarda da shi, kasancewar shi ne abokin mai husumar da ya kai ƙararsa.


Shehul Islami sai da ya share wata goma sha biyu cif a gidan kurkuku  kafin a nemi ya fita, in da shi kuma ya ƙi fita ya ce, sai an bayyana ma sa laifinsa. Daga ƙarshe ya fita daga kurkukun bayan ya cika watanni goma sha biyar da sati biyu da kwana ɗaya bisa ga nacewar wani basaraken garinsu.


Wata bakwai bayan fitowarsa sai aka sake mayar da shi a cikin watan Shawwal na 707H saboda ya ci gaba da zama a Masar mutane na amfana da shi. A wannan karon sai ya kasance mutane suna tururuwa a gidan kaso don gaishe shi da yin fatawa a wurinsa, abin da ya daɗa cinna wutar gaba a tsakaninsa da waɗanda ke bibiyarsa da baƙar aniya. 


Bayan fitowarsa ma, ɗan Taimiyyah bai fasa abin da yake yi na karantarwa da fallasa miyagun aƙidu ba. Wannan ya sa aka ɗauke shi daga Alkahira zuwa Iskandariyya da nufin ya haɗu da ‘yan dabar garin su kashe shi.


Ana haka ne sai aka samu canjin gwamnati lokacin da sarki Muhammad ɗan Kalawun ya sake koma ma kujerar sarauta sai ya mayar da Shehul Islami zuwa hedikwatar ta Masar. Daga nan kuma suka fita a shekarar 712H da nufin yaƙar kafiran Tattar, sai Allah ya mayar da maƙiyan garuruwansu ba tare da an yi yaƙi ba. Don haka, sai Ibnu Taimiyyah ya koma gida Sham, in da ya haɗu da tarba wanda ba a taɓa ganin irinta ba!


Bayan ya yi shekara bakwai da sati bakwai a ƙasar Masar tun wancan kiran da aka yi masa, ko bayan komawarsa gida Shehul Islami ya ci gaba da samun matsaloli da malamai masu ƙaramin sani da taurin kai. Kamar yadda suka yi caa akansa wai don ya ce, in mutum ya yi rantsuwar saki kaffara kawai zai yi, aurensa na nan.


Haka ma don cewar da ya yi saki uku na komawa ɗaya idan an yi su zama guda. Waɗannan malamai ba su samu sukuni ba sai da suka sa aka hana shi fatawa a shekarar 719H. 


A shekara ta 720H aka sake iza ƙeyar babban malamin zuwa gidan kaso in da ya share wata biyar da kwana goma sha takwas. 


A shekara ta 726H wasu Alƙalai sun tsoma bakinsu a cikin rikicin Ibnu Taimiyyah da maƙiyansa, in da aka wallafa wata fatawa ta ƙarya aka jingina ta gare shi, wai ya haramta ziyarar kabarin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da na sauran Annabawa, alhalin shi kuwa ya rarrabe tsakanin ziyararsu ne ita kaɗai da kuma haɗa ta da yin tafiyayya. Ya labarta saɓanin magabata a kanta, sannan ya nuna karkata ga hanawa idan ya kasance an yi tafiyayya saboda ita. Ya kuma bayyana hujjojinsa na ingantattun hadissai. 


Wannan rikicin ma dai sai da ya sake mayar da wannan bawan Allah a gidan maza, in da ya samu damar da ya yawaita wallafe-wallafe gami da bautar Allah Ta’ala. 


A shekara ta 728H aka fitar da duk littafan da ke tare da shi da alkalumma da tawadar da aka samu a wurinsa, saboda wani malami da ake kira Ikhna’i ya kai karar sa, don ya yi ma sa raddi, kuma wai ya jahiltar da shi.


A nan ya zama dole Ibnu Taimiyyah ya haƙura ya duƙufa ga zikiri da sallah da karatun Alkur’ani da yake waɗannan suna a kansa tun zamanin ƙuruciya. 


RASUWARSA 


Ya fara rashin lafiya a farkon Satumba 1328.


Allah ya karɓi ransa a gidan kurkuku na birnin Dimashka ( Damascus Syria 🇸🇾 ) yana da shekaru 67 waɗanda suke cike da karantarwa da haƙuri da jihadi. Ya rasu kafin wayewar garin litinin 20 ga watan Zul Qi’ida 728H. Wanda Yazo dai-dai da 26 Satumba 1328. 


Da wannan labari ya isa ga jama'a, sai aka yi ta nuna goyon bayansa ga jama'a. Bayan da hukumomi suka ba da izini, an ba da rahoton cewa dubban mutane sun zo don nuna girmamawa. Sai suka taru a cikin Kagara suka yi jerin gwano har zuwa masallacin Umayyawa. An gudanar da sallar jana’izar a cikin kagara wanda malami Muhammad Tammam ya yi, kuma an yi na biyu a masallacin. An yi sallar jana’iza ta uku kuma ta ƙarshe ta ɗan’uwan Ibn Taimiyyah, Zainul-Din. An binne shi a Damascus, a Maqbara Sufiyya ("maƙabartar Sufaye"). An binne ɗan uwansa Sharafuddin a maƙabartar da ke gabansa.


An ruwaito cewa maza dubu ɗari biyu da mata dubu goma sha biyar zuwa goma sha shida ne suka halarci sallar jana'izarsa. Ibn Kathir ya ce a tarihin Musulunci, jana'izar Ahmad bn Hanbal ne kaɗai ya samu halartar kamar Wannan taron. 


IYALI 


Bai yi aure ba ballantana ya bar zuri’a. Bai kuma taɓa furta kalma ɗaya da take nuna rashin sha’awarsa ga auren ba. 


To, ko me ya hana shi cin moriyar

wannan Sunnah?


Sanin gaibu sai Allah.


Ɗalibai 


Da yawa daga cikin ɗaliban Ibn Taimiyya sun zama malamai a nasu ɓangaren.  Ɗalibansa sun fito ne daga wurare daban-daban kuma sun kasance a makarantu daban-daban (mahabbai).  Shahararrun ɗalibansa su ne Ibn Qayyim Al-Jawziyya da Ibn Kathir. Sauran ɗalibansa sun haɗa da: 


1, Al-Dhahabi

2, Al-Mizzi

3, Ibn Abdil-Hadi

4, Ibn Muflih

5, ’Imad al-Din Aḥmad al-Wasiti

6, Najm al-Din al-Tufi

7, Al Ba'labakki

8, Al Bazzar

9, Ibn Qadi al-Jabal

10, Ibn Fadlillah al-Amri

11, Muhammad Ibn Al-Manj

12, Ibn Abdus-Salam al-Batti

13, Ibn al-wardi

14, Umar al-Harrani

Monday 30 September 2024

Gajeren Sakon Nuna Amincewar Soyayya Ga Masoyi

Gajeren Sakon Nuna Amincewar Soyayya Ga Masoyi

Ka buɗe mini zuciyarka tare da barka na shiga ciki ta zamo sirrina.


Saƙon Nuna Amincewar Soyayya Ga Masoyi
Hoto: Medium

MarubuciImran Musa Jahun


Tabbas ina son ka a cikin raina, kai kaɗai kake ɗebe mini kewa, idan na ji muryarka.


Ka kewaye dukkan zuciyata gami da ruhina.


Son ka shi ne komai a gare ni.


Muradina gare ka shi ne ka zamo uban yarana.

Abin Da Ya Kamata Sabon Dan Kasuwa Ya Sani

Abin Da Ya Kamata Sabon Dan Kasuwa Ya Sani

Akwai dalilai da yawa na fara kasuwanci. Akwai mutane da yawa waɗanda ba sa son yi wa gwamnati ko kamfani aiki, sun gwammace su samu kuɗi daga abin da ransu yake so, ko nuna irin basira da fasahar su, ko kuma yin arziki da gumin su. Duk da cewa “idan har kana da ƙaton burin yin abu, to za ka iya”, dole na bayyana cewa ƙoƙarin cimma wannan buri yana da haɗari.


Idan har kana da ƙaton burin yin abu. To za ka iya, ƙetare siraɗi a fara sana'a.
Hoto: Ast consulting

MarubuciBello Galadanchi


Dole duk wanda zai ɗauki wannan aniya, sai yana da zuciyar ɗan kasuwa, da ƙarfin hali na ajiye aikin da yake samun albashi, ya fita shi kaɗai, ya tunkari rayuwa mara tabbas. Wasu mutanen kuma na buƙatar a tunzura su, kamar idan aka kori mutum daga aiki, sai a ga ya yi zuciya ya fara sana’a.


A halin yanzu ba kamar lokutan baya ba, matasa da yawa sun rungumi kama sana’a hannu biyu-biyu. Wasu daga cikin su sun laƙanci ilimi da dabarun kasuwanci tun suna da shekaru goma sha wani abu, kuma suna jin daɗin hakan da ‘yancin tafiyar da sana’ar su. 


Sai an yi imani
Hoto: Bates group

Duk da cewa akwai dalilai da yawa na fara kasuwanci, abin da duk wani ɗan kasuwa yake da shi shi ne zuciyar yin kasada. 


Mutane kaɗan ne suke samun nasara a karon farko, kuma dole sai an jajirce koda ana ji ana gani, kasuwancin ba ya tafiya yadda ake so, kuma sai an ci-gaba da bada himma da yin murmushi da kalamai masu daɗi, da haƙuri a gaban kwastomomi da waɗanda suka ba ka jari a duk lokacin da suka ce “a’a”. Yin imani dangane da sana’a na da matuƙar muhimmanci ga nasara. Babu shakka akwai sana’a’o’i da yawa da ba su buƙatar jari mai yawa, amma kusan dukansu na buƙatar ‘yan kuɗi a farko.


Dole sai sabon ɗan kasuwa ya tabbatar wa iyaye da ‘yan uwa, ko abokai, ko banki, ko Oga, ko kuma duk wani wanda shi ne zai bada jari cewa wannan sana’a sahihiya ce, wato za ta haifar da alheri mai yawa, duk da cewa hakan zai iya ɗaukar lokaci.


Ko kun san cewa sai da kamfanin Amazon ya yi shekaru shida kafin ya fara samun riba?