Monday 17 June 2024

Hirar Rabuwa A Tsakanin Masoya

Tura Wannan Zuwa Ga

HUSSAINI: Kamar yadda kika buƙaci na kawo miki dukkan abinda na sani naki, ga shi na dawo miki da shi.


Rabuwar Masoya
Hoto: IBC24


Marubuci:- Hussaini Na Guys


FARIDA: Haka ne ka dawo da su, ga wasiƙunka nan sai ka karɓa.


HUSSAINI: ba zan karɓa ba domin ba na buƙatarsu.


FARIDA: aikuwa ya zama dole ka karɓa domin ba ni da alaƙa yanzu da su.


HUSSAINI: akwai mana domin kin karanta min wasiƙa don haka ba na buƙatar duk abin da kika taɓa karantawa.


FARIDA: oho maka dai gashi idan za ka ɗauka, ka ɗauka ni na yi tafiyata.


HUSSAINI: uhm tsaya kin manta abu guda ɗaya ba ki dawo min da shi ba.


FARIDA: mene ne?


HUSSAINI: zuciyar da kika bi rana kika bi dare kika sace min ita ba tare da na sani ba, ita nake so ki dawo min da abata yanzun nan.


FARIDA: Uhm wato ma kanka ka sani kenan? ni kuma tunanin da ka sani a kanka da yawan zubar da hawayen da na yi a kanka ina so a dawo min da su.


HUSSAINI: uhm ni ne wato na saki kukan ko bayan kin manta rashin lafiyar da na fuskanta duk ta sanadinki ita ma sai a biya ni.


FARIDA: to na ji na yarda zan biya ka amma ka fara cire kanka daga zuciyata duk zan iya biyan ka sauran.


HUSSAINI: ba zan iya ba domin na kafu a cikinta sai dai idan za ki gwada cire kanki.


FARIDA: an ƙi a cire so ma nake na fi da kafuwa.


HUSSAINI: me kika ce?


FARIDA: tunda ba ka ji ba shikenan.


HUSSAINI: to ai na ji ki yi haƙuri to na san kuskurena ne amma ba zan sake ba.


FARIDA: ka gan ka ko, ni dai ka daina ba ni hakuri ko na yi kuka.


HUSSAINI: to na daina dan ba na so daradaran idanun nan naki su koma jajawur.


FARIDA: ka gani za ka fara ko, aina ga dai ka fi ni kyau.


HUSSAINI: Kai!! Lallai ma ai tazarar ki da ni ta wuce a misalta domin idanu sun tabbatar da ke ɗin me kyau ce.


FARIDA: uhm bari na je sai anjima sai mun haɗu ko?


HUSSAINI: uhm to shikkenan ki je ki kwanta, ki sha ruwan sanyi kin ji?


FARIDA: uhm me ya sa?


HUSSAINI: saboda yau na ga faɗan ki.


FARIDA: hhhhh sai an jima ina son ka.


HUSSAINI: ina ƙaunar ki.


To masoya mu kula da zuciyar mu mu kai ta nesa.


Ku ci gaba da kasancewa tare da mu a kodayaushe, don ci gaba da samun zafafan saƙonnin soyayya da kalaman soyayya na saurare da na karantawa.

TURA WANNAN ZUWA GA

Mawallafi: verified_user