Thursday 19 September 2024

Karanta Labarin Jaki Da Damisa Da Zaki

Tura Wannan Zuwa Ga

Gardama ta murtuƙe tsakanin Jaki da Damisa har abin ya kai su ga ɓacin rai. Suka yanke shawarar su je gun Manyan Dawa ya raba musu wannan tankiya.


Labarin Jaki Da Damisa Da Zaki
Hoto: Success minded

MarubuciBukar Mada


Da isarsu sai Jaki ya ce wa Zaki, "Allah ya ba ka nasara don Allah ka raba mana wannan rigima. Na ce wa Damisa ciyawa shuɗiya ce, ita kuma ta dage da cewa koriya ce. A cikinmu wa yake da gaskiya."


Zaki ya dubi Jaki ya ce, "kai ke da gaskiya."


Jaki ya yi tsalle ya buga ƙafa ƙasa ya fashe da dariya, ya harari Damisa ya ce, "to, ga shi nan, ba ki san komai ba sai rigimar banza." Ya hura hanci, ya runtuma a guje cikin daji yana hargowa tare da harbin iska cikin farin ciki.


Bayan ya tafi sai Damisa ta dubi Zaki ta ce, "Allah ya taimake ka, ciyawa fa koriya ce ba shuɗiya ba."


Zaki ya ce, "i, na sani. Ciyawa koriya ce."


Damisa ta ce, "to me ya sa ka ba Jaki gaskiya?"


Zaki ya ce, "bai kamata ga irinki mai ilimi da kwarjini ki tsaya ɓata lokaci wajen gardama da Jaki, wanda bai san inda kansa ke ciwo ba, ga shi garin sakacinki yana shirin raina ki. Sau da yawa wasu kan dage da gardama, ko da kuwa sun san gaskiya, amma su rufe ido dole dai sai an yarda da abin da suka ce. Babban sakarci kuma shi ne nuna sani a inda jahilci ya yanke cibi."


Damisa ta tafi tana jinjina maganar Manyan Dawa. Ta ga kuma lalle abin da ya faɗa gaskiya ne, sakacinta ya sa Jaki ke son raina ta har yana yi mata dariya.


Sai bango ya tsage ƙadangare ke samun wurin shiga. Ba za ta sake yin sakaci kamar wanda ta yi ba, domin kuwa sakaci ne ya sa injin niƙa ya kwance wa turmi zani a kasuwa.

TURA WANNAN ZUWA GA

Mawallafi: verified_user