Monday 21 October 2024

Karanta Hikayar Tajiri Da Ifiritu (1)

Tura Wannan Zuwa Ga

A zamanin da, a wani babban gari, an yi wani babban attajiri, mai yawan dukiya, mai yawan tausayi da taimakon talakawa.


Hikayar Tajiri Da Ifiritu
Hoto: Gutenberg


MarubuciBukar Mada


Wata rana attajirin nan ya fita bayan gari yawo shi kaɗai domin shan iska, sai ya tsaya domin ya huta a ƙarƙashin wata itaciya mai sanyin inuwa. Ya fito da gurasa da dabino da ruwa daga cikin jakarsa, domin ya ci ya kuma sha ruwan kafin ya wuce gaba.


Bayan ya gama cin gurasa sai ya ɗauko dabino yana ci. Yana cikin cin dabinon nan sai ga wani Ifiritu (aljani), mai girman jiki, tamkar itaciyar kuka, mai tsayin gaske, tamkar itaciyar rimi, da jajayen idanu, tamkar garwashin wuta. Ya fito riƙe da takobi a hannunsa, ya ce da wannan attajiri, tashi na kashe ka tamkar yadda ka kashe ɗana.


Tajiri ya ce, “Ta yaya na kashe ɗanka?”


Ifiritu ya ce, “Yayin da ka ci dabino ka yi jifa da ƙwallon ya sami ɗana a kirji har ya faɗi ya mutu. Babu makawa yanzu in ɗau fansa, in kashe ka tamkar yadda ka kashe shi.”


Tajiri ya ce, “Ka sani ya kai wannan Ifiritu akwai bashi mai yawa a kaina. Ka bar ni in tafi gida, tsawon shekara guda, in bai wa dukkan mai haƙƙi haƙƙinsa, sannan in komo nan ka aikata abin da ka yi nufi a kaina, za ka same ni mai cika alkawari, haka Allah ya kaɗɗara.”


Ifiritu ya yarda da bukata tasa.


Tajiri ya komo gida, ya faɗa wa iyalansa da danginsa da abokansa dukkan abinda ya faru da shi, suka yi ta kuka, kuma ya biya dukkan mai bin sa bashi haƙƙinsa. Bayan shekara guda ya koma inda suka haɗu da Ifiritun nan ya zauna yana jiran fitowarsa.


Yana nan zaune yana jiran abinda zai same shi, sai ga wani tsoho tafe, ya na jaye da barewa, da igiya a wuyanta. Ko da tsohon nan ya iso wurin tajirin nan sai ya ce masa, “Bawan Allah, me ya zaunar da kai wannan wuri? Hala ba ka san cewa wannan wuri matattarar aljanu ba ne?”


Tajiri ya kwashe labarinsa da Ifiritu ya faɗa wa tsoho. Tsoho ya ce, haƙiƙa labarinka akwai ban al’ajibi da tausayi a cikinsa. Lalle ba zan bar nan ba sai na ga abinda zai kasance a gare ka. Ya sami wuri ya zauna.


Suna nan zaune, sai ga wani tsoho tafe ya na jaye da karnuka, baƙaƙe guda biyu. Tsoho mai karnuka ya yi sallama gare su. Bayan sun gaisa, ya tambaye su labarin zamansu wannan wuri wanda ya ke matattarar aljanu. Suka faɗa masa abinda ya ke faruwa. Da ya ji haka sai ya ce, lalle ba zan wuce ba har sai na ga abinda zai faru tsakanin Tajirin nan da Ifiritu. Ya sami wuri ya zauna.


Tsohon nan mai karnuka bai gama zaunawa ba, sai kuma ga wani tsoho tafe akan wata alfadara ramammiya. Da tsoho mai alfadara ya iso ya yi musu sallama, suka gaisa sannan ya tambaye su dalilin zamansu a wannan bigire. Suka labarta masa abinda ke faruwa. Shi ma ya ce ba zai wuce ba sai ya ga ƙarshen wannan al’amari. Ya sami wuri ya zauna.


Tajiri da tsofaffi na nan zaune sai suka riƙa jin wata irin hargowa, mai cike da rugugi da tsawa da iska mai tsanani tana kaɗawa, ƙasa kuwa kamar za ta tsage saboda rugugi da ƙugi. Ƙura ta tashi ta murtuƙe ko’ina, ta rufe hasken rana, ba a ganin komai tamkar a tsakiyar dare.


Yayin da hargowar nan ta lafa, ƙura ta yaye wuri ya koma dai dai, sai mutanen nan suka ga Ifiritu a tsaye da takobi zararre a hannunsa, idanunsa jawur tamkar garwashin wuta. Ya fizgo Tajirin nan daga cikinsu ya ce, tashi in kashe ka tamkar yadda ka kashe ɗana, sanyin zuciyata, farin cikin rayuwata.


Tajiri yana kuka yana kururuwa da hargowa, tsofaffin nan su ma suka fashe da kuka domin tausayin Tajiri. Sai tsohon nan na farko, mai barewa ya matso kusa da Ifiritu, ya durƙusa ya ce, “Ya kai wannan Ifiritu, Sarkin Sarakunan aljanu, da za ka tsaya in ba ka labarina da wannan barewa da nake tare da ita, da ka ji labarin abin al’ajabi wanda ba ka taɓa jin irinsa ba, amma sai idan ka yi alkawarin za ka ba ni wani yanki na jinin wannan Tajiri.”


Ifiritu ya ce, “Na yarda idan ka ba ni wannan labari na ga ya kasance abin al’ajabi da mamaki zan ba ka sulusin jinin wannan mutum.”


Tsoho mai barewa ya yi godiya ya fara ba Ifiritu da sauran mutanen da ke wurin labarinsa, da abin da ya kasance a gare shi tare da wannan barewa, kamar haka:


Tsoho na farko, mai barewa ya ce, ka sani ya kai wannan ifiritu, cewa wannan barewa ta kasance ‘yar baffana ce, na aure ta tun tana ƙarama. Mun zauna tsawon shekara talatin da ita amma Allah bai ba mu haihuwa ba. Sai na sayi kuyanga, na mayar da ita sa-ɗaka, Allah kuwa ya sa na haifi ɗa namiji tare da ita. Yaron nan ya kasance kyakkyawa, mai kyawun sura abin so da ƙauna ga kowa.


Bayan yaron nan ya kai shekara goma sha biyar, sai tafiya ta kama ni zuwa wani birni daga cikin birane. Na ɗebi guzuri na dukiya mai yawa domin ban san iyakar kwanakin da zan yi ba a wannan tafiya. Na tafi, na bar ɗana da uwarsa, da kuma matata, 'yar baffana a gida.


Wannan mata tawa, wadda ita ce wannan barewa da kake gani, ya kai wannan ifiritu, ta kasance masaniya akan bokanci da sihiri kala-kala tun tana ‘yar ƙarama. Don haka bayan tafiyata sai ta sihirce yarona ta mayar da shi bajinin sa, uwarsa kuma ta mayar da ita saniya, ta aika da su wurin mai yi mini kiwon dabbobina a daji, aka saka su a cikin garken shanu.


Bayan wani tsawon lokaci na dawo daga tafiyar da na yi, sai ban ga ɗana da uwarsa ba, na tambayi matata inda su ke. Sai ta ce da ni, ai bayan tafiyarka, kuyangarka ta mutu, ɗanka ya gudu ban san inda ya tafi ba. Wannan labari ya sa ni cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya har tsawon shekara guda.


Lokacin da sallar layya ta zo, sai na aika wa makiyayina da ke ƙauye da ya aiko mini da saniya mai ƙiba kuma mai maiƙo domin in yi layya da ita. Wannan mata tawa sai da ta san yadda ta yi dabarar da ta sa makiyayin nan ya aiko mini da sihirtattar saniyar nan, wato kuyangata, uwar ɗana, a matsayin saniyar da zan yanka.


Da aka kawo saniyar, na tashi na cire rigata, na ɗauki wuƙa, bayan an kayar da ita an ɗaure ƙafafunta, na nufe ta da niyyar in yanka ta domin yin layya. Sai ta riƙa kuka da harbe-harbe, kamar za ta yi mini magana, amma babu baki. Sai tausayi ya kama ni, na ba wani yaron gidana wuƙar na ce ya yanka mini ita, ni kuwa na koma cikin ɗaki.


Bayan an yanka saniyar nan, wadda ta kasance kuyangata ce aka sihirce, da aka feɗe ta sai aka tarar ba ta da nama da mai sosai, daga fata sai ƙasusuwa, ni kuwa niyyata in yi layya da dabba mai nama da mai da yawa. Ganin haka sai na sake aika wa makiyayin nan da ya kawo mini wani bajini/bajimi mai nama da mai sosai. Matar nan tawa kuma ta sa aka kawo mini ɗan nan nawa da ta sihirce shi ya zama sa.


Yayin da aka zo da shi, yana gani na, sai ya tsinke igiyar da aka ɗauro shi da ita, ya rugo zuwa gare ni, ya yi kwance a gabana, kuma ya tashi yana kuki yana kuka, yana kewaya ni. Tausayinsa ya kama ni. Na ce, a mayar da shi a zo mini da saniya mai ƙiba da mai. Amma matata kuwa sai ta ce, ka yanka wannan sa domin yana da ƙiba kuma yana da mai sosai. Allah ya sa ban biye shawararta ba, domin tausayin shi ya riga ya kama ni. Aka mayar da shi.


Bayan kwana biyu, ina zaune, sai ga makiyayin nan nawa ya zo wurina, ya ce, ya shugabana, na zo ne in faɗa maka abin farin ciki da albishir. Na ce da shi, na’am, ina saurarenka.


Makiyayi ya ce mini, ya kai maigidana, na kasance ina da wata ‘ya tawa masaniyar sihiri, tun tana ƙarama ta ke a hannun wata tsohuwa, kakarta, wadda ita ce ta koya mata sihiri. Jiya bayan na koma da bajimin san nan da ba ka yanka ba, sai na tarar da ‘yar nan tawa ta zo gida domin bukin Sallah.


Yayin da na shiga da sa gida, ko da ‘yar nan tawa ta gan shi, sai ta rufe jikinta ta ce mini, ya babana, ta yaya za ka shigo mana da namiji, baligi, cikin gida? Bayan kuwa shi ba muharraminmu ba ne? Sai ta fashe da kuka. Na ce da ita, ina namijin da na shigo muku da shi? Sai ta daina kuka, sai kuma na ga tana dariya. Sai na tambayeta, me ya sa ki kuka? Me ya sa kuma yanzu kike dariya?


Ta ce da ni, wannan bajimin da kake tare da shi, ɗan shugabanmu ne, Tajiri, amma an sihirce shi ne, shi da mahaifiyarsa, kuma matar ubansa ce ta sihirce su. Amma abin da ya sa ni kuka shi ne, mahaifinsa ya sa an yanka uwarsa bai sani ba. Amma abin da ya sa ni dariya shi ne, zan iya kuɓutar da shi na mayar da shi ga siffarsa ta mutum, amma sai na yi sharaɗi da mahaifinsa.


Makiyayi ya ci gaba da faɗa mini cewa, na yi al’ajabi gayar al’ajabi, ban yi barci ba har hudowar asuba, domin na zo na sanar da kai wannan labari, ya shugabana.


Yayin da na ji wannan zance na makiyayina, ya kai wannan ifiritu, sai na ce da shi ya tashi maza mu tafi gidansa domin na ji sharaɗin da 'yarsa take so kafin ta mayar mini da ɗana siffarsa ta mutum.


Da muka iso, ‘yar makiyayi ta tare mu da murna, ta gaishe ni cikin ladabi da girmamawa. Da ɗan nan nawa ya gan ni sai ya taso ya zo ya kwanta a gabana. Na ce da ‘yar makiyayi, shin labarin da mahaifinki ya gaya mini ko gaskiya ne. Ta ce, na’am ya shugabana. Wannan bajimi da kake gani ɗanka ne.


Na ce da ita, idan kika kuɓutar da shi zan ba ki dukkan dukiyata da ta ke hannun mahaifinki. Sai ta yi murmushi, ta ce, ka sani ya shugabana, ba ni da kwaɗayi akan dukiyarka, zan kuɓutar da ɗanka amma akan sharuɗɗa guda biyu: Na farko, ka yarda na auri wannan ɗa naka, na biyu ka bar ni in sihirce wadda ta sihirce ɗanka da kuyangarka, ni ma in ɗaureta cikin sihiri tsawon rayuwarta. Idan ka yarda da waɗannan sharuɗɗa, yanzu zan mayar wa ɗanka da siffarsa.


Na ce, na amince da waɗannan sharuɗɗa, kuma na ƙara miki da dukiyar da ke hannun mahaifinki, ‘yar baffana kuwa, watau matata, ki yi duk abin da kika ga dama da ita.


Yayin da ta ji zancena ta ɗauki tasa, ta cika da ruwa, sannan ta yi wasu karance-karance ta tofa a cikin ruwan nan, sannan ta yayyafa wa bajimin sannan, ta ce, idan Allah ya halicce ka, ka kasance bajimi, to ka ci gaba da zama bajimi, idan Allah ya sa sihirce ka aka yi, ka juya ga siffarka ta asali, da yardar Allah Maɗaukakin Sarki. Nan take sai ya juye ya koma mutum, kamarsa ta asali. Na aura masa ‘yar makiyayin nan, ita kuma ce ta sihirce ‘yar baffan nan tawa zuwa wannan barewa da kake gani, ya kai wannan ifiritu.


Idan wannan labari nawa ya kasance mai ban al’ajabi a gareka ina son ka ba ni sulusin jinin wannan Tajiri da ya kashe ɗanka ba tare da ya sani ba.


Ifiritu ya ce, haƙiƙa wannan labari akwai abin al’ajabi a cikinsa, don haka na ba ka sulusin jinin wannan mutum.


DUBA WANNANHikayar Ali Baba Da Barayi Arba'in (1)


Daga nan sai tsoho na biyu mai karnuka ya matso wurin Ifiritu, ya ce ni ma ina da labarin da zan ba ka akan waɗannan karnuka da kake gani, amma sai idan za ka ba ni sulusin jinin wanan mutum.


Ifiritu ya ce, faɗi labarinka mu ji. Tshoho mai karnuka ya fara labarinsa kamar haka:........


Ku ci-gaba da kasancewa tare da mu a kullum don samun ci-gaban wannan ƙayatacciyar hikayar da sauran zafafan hikayoyi duk a kyauta.
TURA WANNAN ZUWA GA

Mawallafi: verified_user