Monday 7 October 2024

Zan Bar Muku Najeriyarku Na Koma Kasata - Fati Niger

Tura Wannan Zuwa Ga

Fati Niger ɗaya ce daga cikin fitattun mawaƙan Kannywood, a ɗaya daga cikin sababbin waƙoƙin ta da ta saki na baya, bayan nan, tana mai nuni da yadda take fama da ƙalubale a zaman ta a Najeriya.


Zan Bar Najeriya Na Koma Ƙasata - Fati Niger

A saboda haka ne take tunatar da masoyan ta da maƙiyanta a fakaice cewa tana da ƙasa, za kuma ta je can amma za ta dawo.


Waƙar mai taken "Fati Fatima Fatiti.".


Ga kaɗan daga cikin wasu baitocin da ke bayyana irin halin da take ciki;


Ba ku zamtowa daidai da ni.


Maƙiyana dole ku bar mini.


Lokacin Allah ke yi da ni.


Ciwuka ba sa rasa magani.


Na riga ni nai nisa tuni, don ko sunana ya kai gurin da ni ma ban je ba.


Sanannen mawaƙin nan na Kannywood Ado Gwanja shi ne ya yi mata amshin waƙar, amshin da ke nuni da yadda yake lallashin ta kan yanayin da ta kasance a ciki.

TURA WANNAN ZUWA GA

Mawallafi: verified_user