Saturday 5 October 2024

Zafafan Darussa 10 Da Ba Za Ku Same Su A Makarantu Ba

Zafafan Darussa 10 Da Ba Za Ku Same Su A Makarantu Ba

Darussan rayuwa 10 waɗanda ba za a koyar da kai a makaranta ba, amma rayuwa za ta sanar da kai.


Darussan rayuwa
Hoto: Orfonline


1. Rayuwa ba gasa ba ce.


Kowa ka gani a rayuwa yana da nasa tafarkin da ƙaddarar wacce ta sha bamban da na sauran mutane. Don haka ka bar haɗa kanka da wani, kowa a rayuwa yana da rabonsa.


2. Lafiyarka ta fi komai muhimmanci.


Ba za a karantar da kai wannan a makaranta ba, amma rayuwa za ta karantar da kai da zafi. Ba ka da wata kadara ko mallaki da ya wuce lafiyarka.


Idan rashin lafiya ya kama ka, duk wani abu da kake yi a baya ba za ka iya yin sa ba, don haka ka kula da lafiyarka yadda ya kamata domin lafiyar mutum ita ce jarinsa.


3. Farin ciki daga zuciya yake


Yawan dukiya, shahara da ɗaukaka, ko jin daɗi duka ba su ke samar da farin ciki ba. Idan kana da wadatar zuci za ka samu farin ciki da kwanciyar hankali wani kuwa duk abin da yake so a rayuwa yana da shi amma duk da haka cikin damuwa yake kwana.


4. Ba kowanne zance a ke tankawa ba.


Idan ka ce za ka tsaya ka jefi duk wani kare da yake haushi a kan hanyarka ba za ka taɓa isa inda kake so ka je ba. Don haka, ba duk abin da aka faɗa ko aka aikata maka za ka tankawa ba.


Wani lokacin shiru shi ne abu mafi dacewa ga wanda yake neman ka da rigima ko faɗa.


5. Ba za ka iya burge kowa ba a rayuwa.


Duk abin da za ka yi wa mutane, sai wasu sun ji haushinka ko sun tsane ka. Ka yi iya ƙoƙarinka don ka zauna da mutane lafiya, amma ka sani duk abin da za ka yi, ba za ka iya burge kowa ba.


Don haka kada ka yi mamaki don wani ya tsane ka ba tare da dalili ba, saboda wasu mutanen a haka ɗabi'arsu take.


6. Lokaci ya fi komai tsada a rayuwa.


Komai yana da lokaci a rayuwa, don haka ka yi komai a lokacinsa. Duk abin da ya kucce/kuɓce maka za ka iya dawo da shi amma banda lokaci. Idan lokaci ya wuce ya wuce kenan har abada. 


7. Abokai na gaskiya suna da wuyar samu.


Mutane da yawa sukan gina abokantaka ne akan amfanuwa ko saboda abin duniya.


Idan Allah Ya azurta ka da aboki ko Ya azurta ki da ƙawa mai kyawun hali kuma wanda yake son ka da alheri, ka riƙe sa da kyau. Abokai na gaskiya suna da wahalar samu.


8. Tafiya ta fi mahimmanci bisa ga masauki.


Idan ka cika damuwa da sakamakon da kake nema, za ka iya rasa darussa masu muhimmanci da akan koya a cikin hanya.


Kafin isa ga masauki ko burin da kake nema, akwai doguwar tafiya wacce take ɗauke da tarin darussa kuma muhimmancinta daidai yake da na wannan burin da kake nema.


9. Gazawa ɓangare ne na nasara.


Duk wani mutumin da ya yi nasara ya taɓa faɗuwa a wani mataki na rayuwarsa. 


Faɗuwa dama ce da take ƙarfafa azamarka da juriyarka kuma ta karantar da kai abubuwa masu yawa da ba za ka sani ba idan da nasara ta zo gare ka kaitsaye.


10. Tunaninka shi ne kamanninka.


Abin da ka yarda da shi game da kanka da kuma duniyar da ke kewaye da kai su ke hukunta zahirin rayuwarka. Don haka domin canza rayuwarka, dole sai ka fara canza tunaninka.


Waɗannan darussa ne masu muhimmanci amma masu hankali kaɗai kan gane.


Allah Ya ganar da mu!


Tushe/Asali: Hausa Motivation

Friday 4 October 2024

Karanta Gajerun Kalaman Soyayya Masu Dadi

Karanta Gajerun Kalaman Soyayya Masu Dadi

Na yi mamakin ganin yadda nake shirin afkawa dajin da ke cike da sarƙaƙiya, dajin da kowa ke tsoronsa, sai dai hankalina ya kwanta ne tun daga lokacin da na gano cewa kina da nutsuwa da girmama mutane, na san za ki kawo guzuri ga mai shirin tunkarar bakin daji mai nisan tafiyar da ba a san iyakarta ba, mai cike da bishiyar farin ciki da ta ƙunci, nishaɗi da ɓacin rai, samun amincewar ki shi ne kaɗai burina.


Gajerun Kalaman Soyayya Masu Daɗi
Hoto: Adobe Stock

Marubuci:- Prince E


Na damu da ke ya kamata ki sani, ni fa zancen ki nake so, lafazin harshenki abin a so ne, 'yan maza na son ki da wawaso, kin ce musu ni za ki so.


Kyakkyawar gimbiya kin sacen zuciya, kin iya soyayya.


To mene ne sirrin? Shin hasken ƙwayar idanunuwan ki ne, ko kyautatawarki gare ni ce? Kallo ɗaya tak na yi miki nan take sai na ji tamkar na dawwama ga kallon kyakkyawar fuskar da na gani, wacce ta haɗo dukkan wasu shikashikai na kyau.


Sannunki sarauniya mai kyawun duniya, kin iya soyayya kamar a ƙasar India.


Haƙiƙa sabo wawan abu ne, bai yi shawara da ni ba lokaci guda na ji na saba da ke tamkar wacce na ɗauki tsawon shekaru muna tare.


Na gaishe ki sarauniyata mai mulkin birnin alƙaryar zinariyar zuciyata.

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (3)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (3)

A tsammanin ta bai isa ya zo wurin ba a wannan lokacin, domin su a abin hawa suke, shi kuwa a ƙasa yake. Tana zuwa ta same shi ya haɗa kai da gwiwa yana ta kiran sunanta, "Laila! Ya Laila!! Ya Laila!!!" Ta ƙaraso wurinsa tana mai cewa, "Ya Majnunun Soyayya ga Lailarka ta iso!!". Duwatsun kusa da na nesa suka ɗauki muryarta tana amo.


Labarin Soyayyar Majnun Da Laila
Hoto: Dynamite of emotions

Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Nan da nan ya zabura zuwa gare ta, yana mai cewa, "Shin da gaske ne Laila ke ce anan?" Ta amsa "Ni ce!" Ya miƙa mata hannu ta riƙe sai suka ji kururuwar mahaifanta suna nemanta domin a ci-gaba da tafiya. Ta juya da hanzari, ya ce, "Haba Laila kada ki tafi ki bar ni da begenki!" Ta ce, "Kar ka damu, idan na dawo za mu haɗu anan."


"Yaushe za ki dawo?" Ya tambaye ta. Ta ce, "Ban san lokacin ba, amma da zarar mun taho zan aika maka." Da haka ta tafi ta bar shi anan. Majnun ya ce a ransa, "idan ta dawo wa za ta aika ya faɗa min? A ina ɗan saƙon zai same ni? Kawai bari na zauna anan ɗin har sai ta dawo." Ya share wuri ya zauna ba shi da wani abinci sai ganyen bishiyar da ke wajen yana shan ruwan da ke ɓuɓɓugowa daga ƙarƙashin dutse. A kullum zancensa shi ne kiran sunan Laila da addu'ar ta dawo ta same shi. A haka har tsiron bishiya ya fito daga 'ya'yan itacen da yake jefarwa, ganyenta ya nannaɗe masa jiki ya zama tamkar bishiyar a jikinsa ta tsiro.


A can garin da su iyayen Laila suka je da ita kuwa, sai wani attajiri ya fito yana son ta da aure. Nan take ya ba wa iyayen raƙuma ɗari gami da wasu kyautuka masu yawa. Da Laila ta ga alamar lallai za a aurar da ita gare shi sai ciwo ya kama ta. Ta yi ta fama, iyayen suka yi nufin komawa gida domin magani alabarshi idan ta warware sai a yi auren. A hanyar su ta dawowa suka sauka a wannan zangon. Duk da tana fama da jinya Laila ta taso zuwa wurin da suka yi alƙawari da Majnun. Ta kusa isa kenan ta gamu da wani mutum ya ce mata, "Yarinya kada ki je wurin nan da kika nufa. Akwai wata fatalwa mai kamar bishiya da ta bayyana."


Kullum tana kiran sunan "Laila, Laila." Da ta ji haka sai ta tabbatar Majnun ne bai tafi ba. Ta ƙarasa wurin da gudu. Yana ganinta ya yi zumbur ya miƙe tsaye yana mai farin ciki, yana cewa "Laila kin cika alƙawari? Laila ke ce kuwa? Laila za ki aure ni??" 


Kasancewar ya jima sosai a zaune ba ya miƙewa, sai jiri ya ɗebe shi, a lokaci guda kuma zuciyarsa ta buga saboda tsanannin farin ciki. Kansa ya gwaru da dutse ya faɗi sumamme.


Laila na ganin irin wannan sadaukantarwa ta kasa haƙurcewa, zuciyarta ta raurawa, ƙirjinta ya yi matuƙar ƙunci. Nan take numfashinta ya ɗauke ta faɗi a wajen sumammiya ita ma.


Kays Majnun shi ne ya fara farfaɗowa daga sumar da suka yi gabaɗayansu, ya yunƙura da zummar isa inda Lailan take amma sai ya kasa yunƙurawar saboda ba kuzari a tare da shi, cikin wata murya ma'abociyar raurawa ya ƙwalawa Laila kira "Laila...!" shirun da ya biyo baya shi ne ya tilasta masa fara jan jiki a kwancen, a hankali yana jan jiki har ya ƙarasa inda Lailar take a kwance a sume.


Cikin ruɗewa da firgici Majnun ya ringa kiran sunan Laila ganin ba ta ko alamar motsi, ya ce "Kada ki tafi ki bar Majnuninki a cikin azabtacciyar rayuwar da gwara mutuwa da ita, kin sani cewa Majnun da son ki yake rayuwa Laila..." ya ƙarashe kalaman nasa da wasu daɗaɗan baitoci:


Rabuwa da ke ba daɗi na ji a jikina.


Kar ki bar ni Lailata domin kuwa ke ce jin daɗina...'


Farin ciki ne mara misaltuwa ya bayyana ƙarara a fuskar Majnun dai-dai lokacin da ya ga Laila ta motsa.


A dai-dai lokacin da Lailar ta motsa har ma ta samu ta zauna, kuma a lokacin ne iyayen Lailar suka ƙaraso wajen da suke, iyayen Lailar suka ruɗe ganin yadda suka ga 'yarsu a wani mawuyacin hali.


Suka ɗauki 'yarsu da zummar tafiya da ita wani garin daban wanda yake da nisa daga wannan nahiyar, ''Laila..." Majnun ya ƙwala mata kira da ƙarfi ganin har sun fara yin nisa daga wajen da suka bar shi a kwancen, ƙwala mata kiran da ya yi shi ne ya yi sanadiyar ƙara dakusar da ɗan ragowar kuzarin da ke tare da shi, don haka yana gama ƙwala mata kiran sai ya kuma kifewa a ƙasa sumamme.


Laila tana ganin hakan sai ta ruɗe, ta kufce daga hannun iyayenta ta rugo izuwa gare shi.


Za mu ci-gaba Insha Allah.

Wednesday 2 October 2024

Dariya Dole: Ma'aurata Da Aljanu

Dariya Dole: Ma'aurata Da Aljanu

Wani Ango ne ya yi sabon aure shi da matarsa suka tare a sabon gida, kullum kafin su kwanta bacci sai ta wanke kwanukan da aka ci abinci, da tukwane gaba-ɗaya, amma idan safiya ta yi gari ya waye sai su ga duk an ɓata kayan da ta wanke, sai su yi ta mamaki ya haka? Me yake faruwa ne?


Ma'aurata Da Aljanu
Hoto: Maple knoll

Sai suka yanke shawarar cewa yau ba za su yi bacci ba sai sun ga mai yin wannan aikin, dare ya yi dare, sai suka ji an fara motsi a cikin gida, sai suka leƙo su ga ko su wane ne, suna leƙowa kuwa sai suka ga wasu irin halittu sun ɗora girki a kan tukunya, cikin minti biyu abinci ya dahu.


Sai aka fara rabo kamar haka;


Ɗauki wannan ka kai wa Ifritu yana ƙasar India.


Kai kuma miƙa wa Turwas yana ƙasar China.


Kai kuma yi sauri ka je ƙasar Masar (Egypt) ka kai wa Sharfayailu.


Karɓi wannan ka miƙa wa ango da amarya na cikin gidan nan, tun da yau sun laɓe suna kallon mu.


Tushe/Asali: Babu hanyar tabbatar da ainihin mamallakin rubutun, saboda rubutun yana yawo ne ba tare da asalin sunan mamallakin shi ba.

Tuesday 1 October 2024

Karanta Ainihin Tarihin Rayuwar Ibn Taimiyya

Karanta Ainihin Tarihin Rayuwar Ibn Taimiyya

Cikakken sunan Ibn Taimiyyah shi ne ' Taqiy al-Din 'Abu al-Abbas 'Ahmad ibn 'Abd al-Hallim ibn 'Abd as-Salam ibn ' Abdullah ibn al-Khiḍr ibn Muḥammad ibn al-Khiyr ibāllīr- ibn al-Khiḥr Ḥarrānī : أحمد بن عبد الحليم بن عبد السلام بن عبد الله بن الخضر بن محمد بن الخضر بن إبراهيم ب اللهن علي بن علي بن بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن عبد السلام .


Ainihin Tarihin Rayuwar Ibn Taimiyya
Hoto: Asharis assemble


MarubuciSaliadeen Sicey


Sunan Ibn Taimiyyah ( ابن تيمية ) ba a saba ganinsa ba ya samo asali ne daga wata mace daga cikin iyalansa saɓanin namiji, wanda al'ada ce ta da a lokacin kuma har yanzu. Laƙabin " Taimiyya " ya fito ne daga kakarsa wacce ake kira Taimiyyah. Ta kasance mai nasiha kuma an yi masa laƙabi da " Ibn Taimiyyah ". Taimiyya ta kasance fitacciyar mace, shahararriyar mai ilimi da taƙawa da sunan Ibn Taimiyya da yawa daga zuriyarta maza ne suka karɓa.


Ibn Taimiyyah, sunan haihuwa Taqī ad-Dīn ʾAḥmad ibn 'Abd al-Hallim ibn 'Abd al-Salam al-Numayrī al-Harrani, malamin Sunna ne, muhaddith, alkali, Salafist kuma masanin siyasa.


Ahmad ɗan Abdulhalimu ɗan Abdussalami ɗan Abdullahi ɗan Haliru ɗan Muhammadu ɗan Haliru ɗan Aliyu ɗan Abdullahi. Ya shahara da sunan Ibnu Taimiyyah saboda kakarsa da ake kira Taimiyyah. Ana kuma ce ma sa “Majduddini”. Sannan ana ce ma sa “Numairi” saboda shi dan kabilar Banu Numairi ne.


Sannan ana ce ma sa kuma “Harrani” saboda Harrana ne garin da aka haife shi. ( Yanzu Garin Yana Cikin Kasar Turkey 🇹🇷).  


Sannan ana ce ma sa “Dimashki” saboda a garin Dimashka ( Damascus Syria 🇸🇾 ) ne ya girma, ya yi karatu. 


ASALINSA


Ibnu Taimiyyah ɗan asalin ƙasar Turkiyya ne. Don an haife shi a garin Harrana wadda take arewa maso gabashin ƙasar ta Turkiyyah.


Haihuwa


An haife shi ne a ranar litinin 10 ga watan Rabi’ul Awwal 661H Wanda Ya zo dai-dai da 22 Janairu 1263, Amma bayan shekaru shida sai iyayensa suka yi hijira daga ƙasar zuwa ƙasar Siriya inda suka sauka a babban birnin Dimashka, hedikwatar Sham.


Dalilin hijirar tasu kuwa shi ne kaucema fitinar ‘yan Tattar waɗanda suka auka ma garuruwan musulmi suka yawaita ɓarna da zubar da jinin bayin Allah. Game da mahaifansa kuwa, shi ɗan gidan malamai ne domin ya sami kansa a tsakanin iyaye da kakanni da ‘yan’uwa ma’abota karatu. A lokacin da za su yi hijira kuwa babu abin da ya wahalar da su kamar littafai da ke tare da su masu ɗimbin yawa, ga shi kuma suna gudun maƙiya.


Al-harran garin da aka Haifi Shaihil Islam Ibn Taimiyya
Hoto: Wikipedia

Ba domin kiyayewar Allah ba ma ba za su tsira da rayukansu zuwa Sham ( Syria 🇸🇾) ba. Isarsu ƙasar Sham ke da wuya mahaifin Ibnu Taimiyyah Shihabuddini ya fara koyarwa da wa’azi a babban masallacin Jum’ah na Dimashka wanda ake kira Al-Jami’ul A’azam masallaci mafi girma. 


Daman shi fitaccen malamin furu’a ne a mazahabar Hambaliyya. Nan take aka shugabantar da shi ga babbar makarantar hadisinnan da aka sani Darul Hadis As-Sukkariyyah, aka kuma ba shi gida a cikin makarantar in da nan ne Ɗansa Ibnu Taimiyyah ya girma. Kafin haka, kakan Ibnu Taimiyyah Majduddini sanannen malami ne da ya yi wallafe-wallafe a fannin hadisi da Usulul Fiqhi  shi ne mawallafin littafin nan na Muntakal Akhbar wanda Imamus Shaukani ya yi wa sharhi a cikin Naulul Audar. Haka ma baffansa Fakhruddini, malami ne fitacce da ya wallafa babban littafin Tafsirin Alqur’ani. 


Shi ne kuma wanda ya gaji Ibnul Jauzi a kujerarsa ta karantarwa da babban mumbarinsa na Bagadaza.


Kuma IbnuTaimiyyah ya yi karatu a wurinsa.


Mahaifa


Harran gunduma ce a gundumar lardin Şanlıurfa a ƙasar Turkiyya. Yanki ne mai faɗin kilomita 96 kuma yana da yawan mazauna 96,072 a lissafin shekarar (2022). Garin Ya na da kusan kilomita 40 (mil 25) kudu maso gabas da Urfa da kilomita 20 (mil 12) daga mashigar kan iyakar Siriya ta Akçakale.


Mahaifar Ibn Taimiyya
Hoto: Onedio

An kafa birnin Harran a wani lokaci tsakanin ƙarni na 25 zuwa 20 kafin haihuwar Annabi isa (AS) (BC), mai yiwuwa ya kafu a matsayin birnin 'yn kasuwa na Sumerian. A tsawon tarihin farko birnin Harran ya girma cikin sauri zuwa babbar cibiyar al'adu, kasuwanci da addini ta Mesopotamiya. Kuma ya sha zama babban birnin lardi sau da yawa a matsayi na biyu mafi muhimmanci ga babban birnin Assuriyawa na Assur da kanta. A lokacin rugujewar Daular Assuriya, Harran ya ɗan yi aiki a matsayin babban birnin ƙarshe na Daular Neo-Assyrian (612-609 BC).


Harran
Hoto: Holy land photos

Daular Mongol ta mamaye birnin a shekara ta 1260 kuma ta lalata kusan dukkan birnin, mutane sun bar garin har shekara zuwa ta 1271. Duk da cewa an bar Harran a matsayin sansanin soja a ƙarƙashin wasu gwamnatoci a baya, amma a cikin ƙarni na biyar da suka wuce an yi amfani da shi azaman wurin zama na wucin gadi ta wurin makiyaya na gida. Al'ummomi Harran sun koma cikin ƙauye na dindindin a cikin shekarun 1840s, amma kwanan nan Harran ya girma zuwa birni na dindindin ta hanyar ci gaban ban ruwa na aikin gona na cikin gida. Harran gundumar Turkawa ce har zuwa 1946, bayan da aka mayar da ita zuwa wani yanki na gundumar Akçakale. Ta dawo da matsayinta na gunduma a cikin shekarar 1987.


Birnin Harran
Hoto: Pinterest

A yau, babban wurin yawon buɗe ido ne na cikin gida. Garin ya shahara musamman da kiwon ƙudan zuma waɗanda ke da alaƙa da gine-ginen da suka riga suka kasance a Harran a zamanin Mesopotamiya ta dā.


Tashinsa da Iliminsa 


Ibnu Taimiyyah ya tashi a gidan ilimi kamar yadda muka gani. Ya kammala hardar Alƙur’ani tun a lokacin ƙuruciya. Sannan ya kula da sanin ilimomin Fiƙihu da Hadisi da Tafsiri da Arabiyyah.


 Tarihin Ibn Taimiyya
Hoto: Usman Abdullah Malik

Ya soma karantarwa da fatawa da rubuta littafai da tattaunawa da malamai Munazara tun bai wuce shekaru 20 Ba. Koda ya cika shekaru 30 an fara yi masa laƙabin Mujtahidi kuma “Mairaya Sunnah”. Yana da matuƙar wuya a iya siffanta baiwar da Allah ya yi wa Ibnu Taimiyyah ta fuskar ilimi. Masu ba da labarinsa na ganin kasawarsu wajen bayyana irin hikimomin da ke tattare da shi ta wannan haujin. An lisafta malaman da ya gurfana a gabansu don ɗaukar karatu aka tarar sun zarce malamai 200.


Akwai kuma littafan da ya karanta su sau da yawa a wurare daban-daban kamar Musnad na Imamu Ahmad. 


Game da nasa littafai shi kuma, Ibnu Taimiyyah ya wallafa sama da littafai hamsin a fannona daban-daban na addini, banda jananan wallafe-wallafensa da aka tara cikin Majmu’ul Fatawa mai sifili talatin da bakwai. 


Ya ishi mai karatu misali abin al’ajabi cewa, duk da yake Ibnu Taimiyyah bai wallafa Tafsirin Alƙur’ani ba, amma malamai daga bisani sun wallafa shi daga cikin littafansa. Ma’ana an tattara wuraren da ya yi sharhi akan ayoyin Alƙur’ani daga ciki littafansa a tsakankanin maganganunsa da kafa hujjojinsa, sai ga shi an samu kusan kammalallen Tafsiri mai Mujalladi huɗu. 


Mujaddadi Ibnu Taimiyyah muna iya cewa, Allah gwanin sarki ya tashi Ibnu Taimiyyah ne a wani lokaci da buƙatar irinsa ta yawaita. Don kuwa a wancan lokaci al’umma tana fama da matsaloli da rikici da tashin hankula na ciki da na waje. Daga cikin gida musulmi na fama da rabuwar kai, da yawaitar ƙungiyoyi da yaɗuwar bidi’ah da raunin ilimin furu’a.


Ga kuma lalacin da ya zo a cikin jama’a da zaluncin sarakuna da kwaɗayin malamai. Tsibbace-tsibbace da bokanci da duba sun zama gama-gari a cikin al’umma. Daga waje kuma ‘yan mishan sun kai ma musulmi farmaki, ‘yan Shi’ah masu kiran kansu Fadimawa sun haɗa kai da su. Sannan ga Tattar sun shelanta mummunan yaƙi da musulunci da musulmi a duk in da suke a wancan lokaci. 


Shaihun musulunci ya fuskanci duka waɗannan matsaloli da nufin magance su. Ya kuma samu taimakon Allah matuƙa a wajen cimma wannan burin nasa.


Mutum ne da aka suffanta shi da kaifin basira da ƙarfin ƙwaƙwalwa, har wasu ma na ganin bai taɓa sanin abu ya manta da shi ba. Yana da ƙarfin tuna ayoyin Alkur’ani da nassoshin hadissai da maganganun malamai na kowane fanni. Don haka ya kasance mai kaifin hujja wadda take yanke wuyan abokin gaba nan take.


Ga shi kuma jarumi da ba ya tsoron ko-ta-kwana. Don haka ba ya da ja da baya ga abin da ya sa gaba. Sannan yana da kwarjini a idon jama’a da kyawawan ɗabi’u da suka daɗa soyar da shi ga mutane. Ga shi mutum mai kishin gaskiya da ƙoƙarin yaɗa ta. Haɗa da halinsa na gudun duniya da rashin kula da jin daɗinta. Irin wannan malami Allah ya ɗora shi a kan kyakkyawar hanya irin ta Annabawa wane irin canji kake tsammanin al’umma ba za ta ci moriyarsa ba ta hanyarsa? 


Ɗan Taimiyyah nan take ya rurrusa aƙidun da suka zame ma musulunci tsutsar goro ta hanyar rubuce-rubucensa da wa’azozinsa da karantarwarsa. Ya kece raini a wajen wargaza aƙidun Yahudawa da na ‘Yan mishan. Ya yi faɗa da ƙungiyoyi mabiyan son zuciya irin mulhidai da zindiƙai da ‘yan Shi’ah da waɗanda suka wuce wuri a Sufanci.


Ya yi kira ga koma ma littafin Allah da Sunnar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ba tare da ta’assubanci ga wani mutum ko ƙungiya ko mazhaba ba. 


Sa’annan ya kira sarakuna da talakawa zuwa ga yaƙar kafirai waɗanda suka keta hurumin musulmi, musamman dai Tattar. Ya kuma fita ya yi yaƙi a matsayin ɗaya daga cikin sojoji. Tare da haka kuma Ibnu Taimiyyah ya kafa wata makaranta da Allah ya yawaita almajiranta tun daga wancan zamani har zuwa yau, kuma tana ci gaba da bunƙasa har a naɗe ƙasa.


Wannan makaranta tasa tana mutunta magabatan Sahabbai da Tabi’ai da waɗanda suka biyo bayansu, da shugabannin mazhabobi, tana kuma la’akari da ra’ayoyinsu da fatawoyinsu baki ɗaya. Tana kuma rinjayar da nassi ingantacce idan ya zo daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a kan maganar kowa kome darajarsa. 


Wannan makaranta dai tana da ɗaruruwan littafai da dubban malamai a cikinta. Dukkaninsu suna jingina kansu ga Sunnah da bin magabata ba ga shi Ibnu Taimiyyah ɗin ba. Jarabawar da Ibnu Taimiyyah ya gamu da ita yana da wuya Allah ya ɗaukaka wani bawansa ba tare da ya gamu da wata jaraba ba a rayuwarsa. Wannan ita ce sunnar Allah ga Annabawa da malamai mutanen kirki.


Shehun musulunci ya gamu da jarabce-jarabce da dama a sakamakon jihadinsa na makami da na alƙalami waɗanda suka dagula ma sa jin daɗin rayuwa. 


Zan faɗi wasu daga cikinsu a takaice kamar yadda suka zo a tarihinsa daga littattafai da dama.


A shekarar 696H ya gamu da ƙyashi daga abokan tafiya, malamai, waɗanda suka ɗauki littafinsa Al-Fatwal Hamawiyyah suka kai ƙararsa da shi a wurin mahukunta. Sun bi duk hanyoyin da suke iyawa wajen murza maganarsa da ba ta irin ma’anar da suke so su jingina ma sa. A wannan lokaci sarki Saifuddin Jagan ya goyi bayan Ibnu Taimiyyah, ya kuma husata da waɗanda suka kafa adawa da shi. Don haka wannan jarrabawa ba ta daɗe ba ta gushe.


A shekarar 705H lokacin da farin jinin Ibnu Taimiyyah ya gama bayyana, bayan an ga rawar da ya taka a yaƙin da aka yi da Tattar, har kuma ya samu kusanci da hukuma abin da ya ba shi damar sa a kawar da wasu ɓarnace-ɓarnace. Nan take sai ƙurjin hassada ya sake tashi a zukatan wasu malamai daga cikin sufaye.


Sai wani malami da ake kira Nasrul Mambiji da wani malami bamalike ana ce ma sa Ibnu Makhluf suka tafi hedikwatar masarauta da ke ƙasar Masar ( Egypt 🇪🇬 ) su ka kai ƙarar Ibnu Taimiyyah suna tuhumar sa da gurɓata aƙidun jama’a.


Suka kafa hujja da littafinsa na Al-Akidatul Wasiziyyah. A nan ma sarki ya ba da umurni aka zaunar da shi tare da manyan malamai in da aka karance littafin nasa, daga ƙarshe kuma aka barrantar da shi daga saɓa ma magabata.


Sai ma a wannan karon ya samu takardar yabo daga Sarkin Musulmi. Wata ɗaya bayan faruwar wannan, sai waɗannan malaman suka sa sarki ya rubuta ma sa wata takarda ana neman sa da zuwa Misra ( Egypt 🇪🇬) don ya bayyana a gaban sarki. A wannan karon da tuhumar yana neman sarauta! 


An dai zaunar da shi a gaban Ibnu Makhluf don ya yanke ma sa hukunci, abin da ɗan Taimiyyan ya ƙi yarda da shi, kasancewar shi ne abokin mai husumar da ya kai ƙararsa.


Shehul Islami sai da ya share wata goma sha biyu cif a gidan kurkuku  kafin a nemi ya fita, in da shi kuma ya ƙi fita ya ce, sai an bayyana ma sa laifinsa. Daga ƙarshe ya fita daga kurkukun bayan ya cika watanni goma sha biyar da sati biyu da kwana ɗaya bisa ga nacewar wani basaraken garinsu.


Wata bakwai bayan fitowarsa sai aka sake mayar da shi a cikin watan Shawwal na 707H saboda ya ci gaba da zama a Masar mutane na amfana da shi. A wannan karon sai ya kasance mutane suna tururuwa a gidan kaso don gaishe shi da yin fatawa a wurinsa, abin da ya daɗa cinna wutar gaba a tsakaninsa da waɗanda ke bibiyarsa da baƙar aniya. 


Bayan fitowarsa ma, ɗan Taimiyyah bai fasa abin da yake yi na karantarwa da fallasa miyagun aƙidu ba. Wannan ya sa aka ɗauke shi daga Alkahira zuwa Iskandariyya da nufin ya haɗu da ‘yan dabar garin su kashe shi.


Ana haka ne sai aka samu canjin gwamnati lokacin da sarki Muhammad ɗan Kalawun ya sake koma ma kujerar sarauta sai ya mayar da Shehul Islami zuwa hedikwatar ta Masar. Daga nan kuma suka fita a shekarar 712H da nufin yaƙar kafiran Tattar, sai Allah ya mayar da maƙiyan garuruwansu ba tare da an yi yaƙi ba. Don haka, sai Ibnu Taimiyyah ya koma gida Sham, in da ya haɗu da tarba wanda ba a taɓa ganin irinta ba!


Bayan ya yi shekara bakwai da sati bakwai a ƙasar Masar tun wancan kiran da aka yi masa, ko bayan komawarsa gida Shehul Islami ya ci gaba da samun matsaloli da malamai masu ƙaramin sani da taurin kai. Kamar yadda suka yi caa akansa wai don ya ce, in mutum ya yi rantsuwar saki kaffara kawai zai yi, aurensa na nan.


Haka ma don cewar da ya yi saki uku na komawa ɗaya idan an yi su zama guda. Waɗannan malamai ba su samu sukuni ba sai da suka sa aka hana shi fatawa a shekarar 719H. 


A shekara ta 720H aka sake iza ƙeyar babban malamin zuwa gidan kaso in da ya share wata biyar da kwana goma sha takwas. 


A shekara ta 726H wasu Alƙalai sun tsoma bakinsu a cikin rikicin Ibnu Taimiyyah da maƙiyansa, in da aka wallafa wata fatawa ta ƙarya aka jingina ta gare shi, wai ya haramta ziyarar kabarin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da na sauran Annabawa, alhalin shi kuwa ya rarrabe tsakanin ziyararsu ne ita kaɗai da kuma haɗa ta da yin tafiyayya. Ya labarta saɓanin magabata a kanta, sannan ya nuna karkata ga hanawa idan ya kasance an yi tafiyayya saboda ita. Ya kuma bayyana hujjojinsa na ingantattun hadissai. 


Wannan rikicin ma dai sai da ya sake mayar da wannan bawan Allah a gidan maza, in da ya samu damar da ya yawaita wallafe-wallafe gami da bautar Allah Ta’ala. 


A shekara ta 728H aka fitar da duk littafan da ke tare da shi da alkalumma da tawadar da aka samu a wurinsa, saboda wani malami da ake kira Ikhna’i ya kai karar sa, don ya yi ma sa raddi, kuma wai ya jahiltar da shi.


A nan ya zama dole Ibnu Taimiyyah ya haƙura ya duƙufa ga zikiri da sallah da karatun Alkur’ani da yake waɗannan suna a kansa tun zamanin ƙuruciya. 


RASUWARSA 


Ya fara rashin lafiya a farkon Satumba 1328.


Allah ya karɓi ransa a gidan kurkuku na birnin Dimashka ( Damascus Syria 🇸🇾 ) yana da shekaru 67 waɗanda suke cike da karantarwa da haƙuri da jihadi. Ya rasu kafin wayewar garin litinin 20 ga watan Zul Qi’ida 728H. Wanda Yazo dai-dai da 26 Satumba 1328. 


Da wannan labari ya isa ga jama'a, sai aka yi ta nuna goyon bayansa ga jama'a. Bayan da hukumomi suka ba da izini, an ba da rahoton cewa dubban mutane sun zo don nuna girmamawa. Sai suka taru a cikin Kagara suka yi jerin gwano har zuwa masallacin Umayyawa. An gudanar da sallar jana’izar a cikin kagara wanda malami Muhammad Tammam ya yi, kuma an yi na biyu a masallacin. An yi sallar jana’iza ta uku kuma ta ƙarshe ta ɗan’uwan Ibn Taimiyyah, Zainul-Din. An binne shi a Damascus, a Maqbara Sufiyya ("maƙabartar Sufaye"). An binne ɗan uwansa Sharafuddin a maƙabartar da ke gabansa.


An ruwaito cewa maza dubu ɗari biyu da mata dubu goma sha biyar zuwa goma sha shida ne suka halarci sallar jana'izarsa. Ibn Kathir ya ce a tarihin Musulunci, jana'izar Ahmad bn Hanbal ne kaɗai ya samu halartar kamar Wannan taron. 


IYALI 


Bai yi aure ba ballantana ya bar zuri’a. Bai kuma taɓa furta kalma ɗaya da take nuna rashin sha’awarsa ga auren ba. 


To, ko me ya hana shi cin moriyar

wannan Sunnah?


Sanin gaibu sai Allah.


Ɗalibai 


Da yawa daga cikin ɗaliban Ibn Taimiyya sun zama malamai a nasu ɓangaren.  Ɗalibansa sun fito ne daga wurare daban-daban kuma sun kasance a makarantu daban-daban (mahabbai).  Shahararrun ɗalibansa su ne Ibn Qayyim Al-Jawziyya da Ibn Kathir. Sauran ɗalibansa sun haɗa da: 


1, Al-Dhahabi

2, Al-Mizzi

3, Ibn Abdil-Hadi

4, Ibn Muflih

5, ’Imad al-Din Aḥmad al-Wasiti

6, Najm al-Din al-Tufi

7, Al Ba'labakki

8, Al Bazzar

9, Ibn Qadi al-Jabal

10, Ibn Fadlillah al-Amri

11, Muhammad Ibn Al-Manj

12, Ibn Abdus-Salam al-Batti

13, Ibn al-wardi

14, Umar al-Harrani

Monday 30 September 2024

Gajeren Sakon Nuna Amincewar Soyayya Ga Masoyi

Gajeren Sakon Nuna Amincewar Soyayya Ga Masoyi

Ka buɗe mini zuciyarka tare da barka na shiga ciki ta zamo sirrina.


Saƙon Nuna Amincewar Soyayya Ga Masoyi
Hoto: Medium

MarubuciImran Musa Jahun


Tabbas ina son ka a cikin raina, kai kaɗai kake ɗebe mini kewa, idan na ji muryarka.


Ka kewaye dukkan zuciyata gami da ruhina.


Son ka shi ne komai a gare ni.


Muradina gare ka shi ne ka zamo uban yarana.

Abin Da Ya Kamata Sabon Dan Kasuwa Ya Sani

Abin Da Ya Kamata Sabon Dan Kasuwa Ya Sani

Akwai dalilai da yawa na fara kasuwanci. Akwai mutane da yawa waɗanda ba sa son yi wa gwamnati ko kamfani aiki, sun gwammace su samu kuɗi daga abin da ransu yake so, ko nuna irin basira da fasahar su, ko kuma yin arziki da gumin su. Duk da cewa “idan har kana da ƙaton burin yin abu, to za ka iya”, dole na bayyana cewa ƙoƙarin cimma wannan buri yana da haɗari.


Idan har kana da ƙaton burin yin abu. To za ka iya, ƙetare siraɗi a fara sana'a.
Hoto: Ast consulting

MarubuciBello Galadanchi


Dole duk wanda zai ɗauki wannan aniya, sai yana da zuciyar ɗan kasuwa, da ƙarfin hali na ajiye aikin da yake samun albashi, ya fita shi kaɗai, ya tunkari rayuwa mara tabbas. Wasu mutanen kuma na buƙatar a tunzura su, kamar idan aka kori mutum daga aiki, sai a ga ya yi zuciya ya fara sana’a.


A halin yanzu ba kamar lokutan baya ba, matasa da yawa sun rungumi kama sana’a hannu biyu-biyu. Wasu daga cikin su sun laƙanci ilimi da dabarun kasuwanci tun suna da shekaru goma sha wani abu, kuma suna jin daɗin hakan da ‘yancin tafiyar da sana’ar su. 


Sai an yi imani
Hoto: Bates group

Duk da cewa akwai dalilai da yawa na fara kasuwanci, abin da duk wani ɗan kasuwa yake da shi shi ne zuciyar yin kasada. 


Mutane kaɗan ne suke samun nasara a karon farko, kuma dole sai an jajirce koda ana ji ana gani, kasuwancin ba ya tafiya yadda ake so, kuma sai an ci-gaba da bada himma da yin murmushi da kalamai masu daɗi, da haƙuri a gaban kwastomomi da waɗanda suka ba ka jari a duk lokacin da suka ce “a’a”. Yin imani dangane da sana’a na da matuƙar muhimmanci ga nasara. Babu shakka akwai sana’a’o’i da yawa da ba su buƙatar jari mai yawa, amma kusan dukansu na buƙatar ‘yan kuɗi a farko.


Dole sai sabon ɗan kasuwa ya tabbatar wa iyaye da ‘yan uwa, ko abokai, ko banki, ko Oga, ko kuma duk wani wanda shi ne zai bada jari cewa wannan sana’a sahihiya ce, wato za ta haifar da alheri mai yawa, duk da cewa hakan zai iya ɗaukar lokaci.


Ko kun san cewa sai da kamfanin Amazon ya yi shekaru shida kafin ya fara samun riba?

Sunday 29 September 2024

Gajerun Kalaman Sanyaya Zuciyar Masoyiya

Gajerun Kalaman Sanyaya Zuciyar Masoyiya

Kar ki manta da ni a rayuwarki, haka ni ma zalika duk rintsi kina raina.


Kalaman Sanyaya Zuciyar Masoyiya
Hoto: Discover hubpages

MarubuciImran Musa Jahun


Na miƙa mukullin zuciyata gare ki, ki buɗe min zuciyarki na cike dukkan guraban da suke marhabin da ni, wanda ba wani mahaluki da zai iya mallakar zuciyarki idan ba ni ba.


Ki ce mini ni ne naki na har abada, ni ma zan ce hakan don mu kasance cikin jin daɗin duniya.


Ma'anar kalmar ina son ki (I LOVE YOU).


I = Na sallama, ke ma ki sallama

mini zuciyarki.


L = Ji! Ni ne irin wanda za a so.


O = Lura sannan ki bari na samu gurbi a zuciyarki.


V = Tabbas ina son ki tawa.


E = Kin kewaye dukkan zuciyata.


Y = Son ki shi ne nawa farin cikin.


O = Ki buɗe ƙofar zuciyarki na shiga.


U = Kafin na shigo ki mini kyakkyawan gurbi a cikin zuciyarki.


Ki tuna fa cewa duk inda ya zama ba so, duniya za ta zama cikin halin ƙunci na ba ranar da za ta daina, rayuwa za ta zama mara amfani gare mu, mutane za su kasance cikin rashin zaman lafiya a tare da su.


So shi ne sirrin rayuwarmu.


So shi ne farin cikin mu da nasarorinmu na rayuwa.


Na sallama zuciyata gami da ruhina gare ki.


So shi ne ya haɗa komai da komai na jin daɗin duniya, saboda Adamunmu shi da Hauwa'u sun zamo uwa gare mu tunda tsatsanmu ya zo ɗaya, mu daina ƙin junanmu.


Ku kasance da ni zan ci gaba da nishaɗantar da ku a kodayaushe.

Kalma Daya Mai Ma'anoni Da Yawa A Hausa

Kalma Daya Mai Ma'anoni Da Yawa A Hausa

Gammo (Na kifi).

Gammo (Na itace).

Gammo (Na daukar Kaya).


Kalma Daya Mai Ma'anoni Da Yawa A Hausa
Hoto: Banter speech



Iska (Aljani).

Iska ( da ake Shaƙa).

Iska (Tusa).

Iska (Iskanci.. hahaha).

Kyauta (Suna).

Kyauta (bada wani abu/tukwici).

Mai (na gyada).

Mai (na kwakwa).

Mai (na fetur).

Mai (Kalanzir).

Mai (na nama).

Mai (na inji).

Mai ( na jirgi).

Kaya ( na tsiro da akan taka).

Kaya (ta kifi).

Kaya (na kafiya ko naci).

Mai gida ( Uba).

Mai gida (Miji).

Mai gida (Shugaba ko jagora).

Laushi (Na fata).

Laushi (Na hali).

Laushi (Na gajiya).

Laushi (Na Rashi).

Kura ( Dabba).

Kura ( Ta jawo guga).

Kura (Ta Turawa).

Kura-kura (Abu guda-guda).

Kura (Ta iska).

Kura (Sa ido Misali "ƙura ido).

Saturday 28 September 2024

Karanta Tarihin Rayuwar Hassan Nasrallah

Karanta Tarihin Rayuwar Hassan Nasrallah

An haifi Sheikh Hasan Nasrallah ne dai a ƙauyen Karanteena na ƙasar Labanon, a Ranar 31 Ga Watan Augusta 1960, mahaifinsa kuwa ɗan kasuwa ne mai sayar da 'ya'yan itace don amfanin al'ummar yankin tare da yayan Nasrallah ɗin, a wasu lokuta kuma Shiekh Hasan shi ma ya kan je wajensa don taimaka masa. A irin wannan zuwa da yake yi ne wata rana ya ga hoton Imam Musa al-Sadr, sanannen malamin nan na ƙasar Labanon ɗin da ya ɓace a ƙasar Libya kuma har ya zuwa yanzu ba a san inda yake ba, wannan hoto dai ya yi tasirin gaske a zuciyar Nasrallah inda har ya yi fatan shi ma da a ce wata rana zai zamanto kamar wannan malami da kuma fatan ya kasance daga cikin mabiyansa saboda irin haiba da alamun taƙawa da ke tattare da shi.


Tarihin Rayuwar Hassan Nasrallah
Hoto: Aljazeera

MarubuciSaliadeen Sicey


Hassan Nasrallah dai tun yana ƙarami bai kasance kamar sauran yaran ƙauyen nasu da suke zuwa wasan ƙwallo, iyo da dai sauransu ba, saɓanin haka ya kasance ya kan lizimci zuwa masallaci duk da cewa shi dai ba shi da alaƙa da wani malami na musamman, amma dai duk da haka ya kasance mai kula da al'amuran addini. Irin wannan yanayi nasa ne ma ya sanya ya kan zauna shi kaɗai tare da hoton Imam Musa al-Sadr saboda mafi yawan al'ummar garin ba su damu da lamuran addini ba.


Lokacin da ya ɗan data, wato kimanin shekaru tara a duniya, Shiekh Hasan ya kan je wata 'yar kasuwa da ake sayar da gwanjon littattafai don ya saya da kuma karantawa, musamman ma dai littattafan da suka shafi addini, duk da cewa dai ba ya fahimtar dukkan abin da ya karanta saboda ƙarancin shekaru, to amma dai ya kan ajiye waɗannan littattafan da nufin cewa nan gaba zai sake karanta su da kuma fahimtar abin da suka ƙunsa. A daidai wannan lokaci da Nasrallah ya ke ci gaba da wannan bincike yana makarantar elementare ne a makarantar al-Najah da ke yankin nasu. A shekarar 1970 ne dai ya gama wannan makaranta da kuma shiga makaranta ta gaba a Sinelfeel da ke garin Sur. Bai dai samu ya gama wannan makaranta ba saboda ɓarkewar yaƙi a ƙasar Labanon ɗin a shekarar 1975, lamarin da ya tilasta wa iyalansa barin wannan gari da komawa ƙauye.


Hassan Nasrallah ya fara shiga wata ƙungiya ce dai a lokacin da ya koma garin Bazouriya inda ya shiga cikin ƙungiyar Amal ta Imam Musa al-Sadr saboda irin alaƙa da kuma ƙaunar da ya ke wa Imam Musa ɗin a lokacin kuwa yana ɗan shekara 15 ne a duniya, ita dai wannan ƙungiyar ta Amal ana mata laƙabi da "Ƙungiyar Marasa Galihu", duk da cewa a wannan gari nasu dai ƙungiyoyin kwaminisanci da Markisanci ne suka fi samun gindin zama. Bayan zamansa ɗan ƙungiyar Amal tare da wansa Husain Nasrallah, an ba shi matsayin wakilin ƙungiyar na wannan gari duk kuwa da ƙarancin shekarun da ya ke da shi.


Bayan ɗan wani lokaci dai, Hasan Nasrallah ya ƙudiri aniyar tafiya birnin Najaf al-Ashraf na ƙasar Iraki don karatun addinin Musulunci a lokacin kuwa yana ƙasa da shekaru 16 ne a duniya. Bayan da ya yi wannan ƙuduri sai ya tafi garin Sur inda ya sadu da wani malami da ke wakiltar Imam Musa al-Sadr a garin mai suna Sayyid Muhammad al-Garawi don tattaunawa da shi kan yadda zai cimma wannan buri nasa na tafiya garin Najaf ɗin. Jin haka sai Sayyid al-Garawi, wanda daman yana da alaƙa da kuma sanayya da Shahid Sayyid Muhammad Bakir al-Sadr, babban malamin garin Najaf ɗin na lokacin, sai ya rubuta wa Shahid al-Sadr ɗin wasiƙa da bayyana masa irin ƙwazon Nasrallah don ya ba shi daman karatu a Najaf ɗin.


Bayan 'yan shirye-shirye, sai Hassan Nasrallah ya yi bankwana da iyalansa ya kama hanyar Najaf, koda ya isa sai ya tafi inda 'yan ƙasar Labanon su ke da nufin su taimaka masa isar da wasiƙar da take tare da shi ga Shahid al-Sadr, inda Sayyid Abbas Musawi, wanda daga baya ya zamanto shugaban Hizbulllah, ya karɓi wasiƙar da nufin isar da ita zuwa ga mai ita, wannan dai ita ce farkon alaƙar Nasrallah da Sayyid Abbas al-Musawi. Bayan isar da wannan wasiƙa dai, Shahid al-Sadr ya yi maraba da Hassan Nasrallah, inda ya buƙaci Sayyid Abbas al-Musawi da ya sama masa wajen zama da kuma ci gaba da koyar da shi, ta haka ne Sayyid Abbas al-Musawi ya zamanto malami kana kuma mai shiryar da Sayyid Nasrallah, wannan alaƙa da ta ci gaba da wanzuwa har lokacin da Sayyid Abbas din ya yi shahada lokacin da sojojin yahudawan sah-yoniya suka kai masa hari da tarwatsa motar da yake ciki.


Da yake Sayyid Abbas ya yi nisa a karatunsa a lokacin, don haka sai Shahid al-Sadr ya ware masa aji don koyar da ƙananan ɗalibai, inda daga cikin ɗaliban har da shi Nasrallah. Saboda irin ƙwazon da Sayyid Abbas ya ke da shi ya sanya ɗaliban nasa sun yi karatu mai yawan gaske cikin ɗan karamin lokaci.


A shekarar 1978 Nasrallah ya gama kashin farko na karatun nasa yana mai shauƙin ci gaba da karatunsa a wajen wannan malami nasa da ya kasance masa tamkar uba, to sai dai kuma wani gagarumin al'amari ya faru da ya kusan kawo ƙarshen wannan karatu nasa. Wannan lamari kuwa shi ne faruwar wani gagarumin shiri da gwamnatin Iraki ta wancan lokaci ta fara na korar ɗaliban Hawza 'yan ƙasashen waje da suke karatu a Irakin suna masu zargin wasu da kasancewa jami'an leƙen asirin ƙasar Siriya wasu kuma suna da alaƙa da wasu ƙungiyoyin Musulunci.


Wannan lamari ne dai ya sa jami'an tsaron Irakin suka kai hari ga makarantar Hawza ta birnin Najaf da kame wasu ɗalibai, inda bayan tsare su na wani lokaci suka kore su da dama kuwa daga cikinsu 'yan ƙasar Labanon ne. A daidai lokacin da jami'an gwamnatin Saddam ɗin suka zo kame ɗaliban kuwa, Sayyid Abbas Musawi ba ya cikin ƙasar Iraki ya tafi hutu Labanon don haka aka shawarce shi da kada ya dawo don ana nemansa ruwa a jallo. A nasa ɓangaren shi ma Nasrallah ba ya makarantar lokacin da aka zo wannan kame, don haka bayan da ya dawo aka gaya masa labarin kame 'yan'uwansa, sai aka shawarce shi da shi ma ya gudu, inda kafin jami'an tsaron su ankara ya samu damar ficewa daga Irakin da kuma komawa gida.


Bayan komawarsa gida ma, Nasrallah ya ci gaba da karatunsa a wajen Sayyid Abbas Musawi a makarantar da ya buɗe, a daidai lokacin da kuma ya ke karantarwa a ita dai wannan makaranta. Baya ga karatu da kuma karantarwar, Sayyid Nasrallah ya ci gaba da gudanar da ayyukansa a wannan kungiya ta Amal, inda ma aka zaɓe shi a matsayin wakilin ƙungiyar na ɓangaren siyasa a garin Bikaa.


A shekarar 1982, bayan mamayan da ƙasar Isra'ila ta yi wa ƙasar Labanon, an samu kafuwar wasu ƙungiyoyi masu son fada da wannan mamaya, to sai dai kuma saboda wasu dalilai da suka yi ta bijirowa ya sanya an samu rabuwar kai tsakanin 'yan wannan ƙungiya ta Amal, inda wasu daga cikinsu suka fice suka kafa ƙungiyar Hizbullah daga cikin waɗanda suka ɓalle ɗin kuwa har da Sayyid Nasrullah. Babban take da burin ƙungiyar Hizbullah ɗin dai shi ne kawo ƙarshen wannan mamaya ta yahudawa.


Duk da cewa dai daga farko-farkon lamurra Hasan Nasrallah bai kasance daga cikin majalisar gudanarwa ta wannan ƙungiya ta Hizbullah ba, to sai dai kuma ya riƙe muƙamai daban-daban a ƙungiyar da suka haɗa da shugaban reshen Ba'alabak daga baya kuma ya zamanto shugaban reshen Bika'a na ƙungiyar gwagwarmayar. Sannan kuma ya kasance mataimakin shugaban ƙungiyar reshen birnin Beirut, daga baya ma dai ya zamanto shugaban reshen Beirut ɗin bayan da shugaban reshen Sayyid Ibrahim Ameen Sayyid ya koma ɓangaren siyasa na ƙungiyar, hakan ya sanya ya kasance daga cikin manyan jami'an ƙungiyar na gaba-gaba. Duk da cewa dai Sayyid Hassan na son ci gaba da karatunsa, to sai dai kuma saboda wannan mamaya na yahudawa ya hana shi hakan saboda ayyukan fada da wannan mamaya. To amma a shekarar 1989, bayan samun izini daga ƙungiyar, Nasrallah ya nufi birnin Kum na ƙasar Iran don ci gaba da karatun nasa. A garin Kum dai Nasrallah ya yi karatu a wajen malamai daban-daban inda duk suke yaba masa saboda irin ƙwazon da ya ke da shi.


To sai dai kuma wannan karatu nasa a Kum bai jima ba saboda kisan gillar da yahudawan sahyoniya suka yi wa Sayyid Abbas al-Musawi, shugaban ƙungiyar ta Hizbullah a shekarar 1992, wannan ɗanyen aiki dai ya tilasta masa dawowa gida. Bayan jana'iza da zaman makoki dai majalisar gudanarwa ta ƙungiyar Hizbullah ɗin ta zaɓi Sayyid Hassan Nasrullah a matsayin shugabanta, saboda irin ƙwazonsa da kuma kusancin da yake da shi da Shahid Abbas al-Musawi, kuma wannan muƙami ne ya ke ci gaba da riƙewa har zuwa lokacin kashe shi.


Hassan Nasrullah dai ya yi aure ne a shekarar 1978, inda ya auri Fatima Yasin wacce ta fito daga garin al-Abbasiya da ke yankin Sur. Ya zuwa yanzu dai Sayyid Nasrallah yana da 'ya'ya huɗu, wato Hadi, wanda ya yi shahada a yayin bata kashi da sojojin  ƙasar Isra'ila a lokacin yana ɗan shekaru 18 a duniya, sai kuma mai biye masa wato Muhammad al-Jawad, sai kuma Zainab sai kuma na ƙarshensu Muhammad Ali.


Kisan Ɗan Nasa Muhammad hadi


A daren 12/13 ga watan Satumban shekarar 1997 aka kashe mayaƙan Hizbullah huɗu a wani harin kwantan ɓauna da Isra'ila ta kai kusa da Mlik. Ɗaya daga cikin waɗanda suka mutu shi ne Muhammad Hadi mai shekaru 18, babban ɗan Nasrallah. Sojojin Lebanon biyar da wata mace sun mutu a wani harin da aka kai ta sama a lokaci guda a arewa da 'yankin tsaro'. Ana kallon hare-haren a matsayin martani ga farmakin da aka kai mako guda da ya gabata inda aka kashe kwamandojin Isra'ila goma sha biyu. An ruwaito Nasrallah yana cewa yayin da yake samun labarin rasuwar ɗansa "Ina alfahari da kasancewa mahaifin ɗaya daga cikin shahidai."


Daya Cikin Maganganunsa


"Idan har za mu kori mamayar Isra'ila daga ƙasarmu, ta yaya za mu yi haka? Mun lura da abin da ya faru a Falasɗinu, a Yammacin Gaɓar Kogin Jordan, da Zirin Gaza, da Tuddan Golan, da Sinai, mun cimma matsaya kan cewa, ba za a iya dogaro da ƙasashen Larabawa ba, ko kuma Majalisar Ɗinkin Duniya ....Hanya ɗaya tilo da muke da ita ita ce mu ɗauki makamai mu yaƙi dakarun mamaya."


A wata hira da jaridar Washington Post, a shekara ta 2000, Nasrallah ya ce "Ni ina adawa da duk wani sulhu da Isra'ila. Ban ma yarda da kasancewar wata ƙasa da ake kira 'Isra'ila ba." Ina ganin kasancewarsa a matsayin rashin adalci da kuma haramun, shi ya sa idan Lebanon ta ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya da Isra'ila, kuma ta kawo wa majalisar dokoki hakan, wakilanmu za su yi watsi da ita, Hizbullah ta ƙi amincewa da duk wani sulhu da Isra'ila bisa manufa."


A shekara ta 2006, Nasrallah ya ce "Babu mafita ga rikici a wannan yanki face ɓacewar Isra'ila."


Da yake magana a ranar Kudus a ranar 2 ga Agusta, 2013, Nasrallah ya ce Isra'ila "ƙasar daji ce da dole ne a kawar da ita."


An yi zargin yunƙurin kashe Shi a shekarar 2008


Almalaf, majiyar labaran Iraki a ranar 15 ga watan Oktoban 2008, ta naƙalto majiyoyi daga ƙasar Lebanon na cewa an sakawa shugaban ƙungiyar Hizbullah Hasan Nasrallah guba a makon da ya gabata, kuma likitocin Iran da suka je Labanon domin yi masa magani sun cece shi. Majiyar ta shaida wa jaridar cewa an yi amfani da wani sinadari mai guba musamman kan shugaban mayaƙan na Shi'a. Da alamu dai yanayin lafiyarsa ya yi tsanani na tsawon kwanaki har sai da likitocin Iran suka zo suka yi nasarar ceto rayuwarsa. Almalaf ya yi iƙirarin cewa majiyoyin sun yi imanin cewa akwai yiwuwar sanya gubar wani yunƙuri na kashi da Isra'ila ta shirya ne.


Hezbollah ta musanta cewa an saka wa Nasrallah guba. Ɗan majalisar dokokin ƙasar Labanon Al-Hajj Hassan ɗan ƙungiyar Hizbullah ya ce: "Wannan ƙarya ce da ƙage-ƙage, gaskiya ne ban ga Nasrallah a cikin makon da ya gabata ba, amma ba shi da lafiya." Likitocin na Iran sun isa ne a ranar Lahadin da ta gabata da misalin ƙarfe 11:00 na dare, bisa dukkan alamu cikin wani jirgin soji na musamman. A cewar jami'an Almalaf sun yi la'akari da tashin Nasrallah zuwa Iran don ci gaba da jinya.


Mutuwa


A ranar 27 ga Satumba, 2024, sojojin saman Isra'ila sun kai wani hari ta sama kan hedkwatar Hezbollah da ke Beirut, wanda aka ce sun nufi Nasrallah. Aƙalla mutane shida ne suka mutu sannan sama da 90 suka jikkata sakamakon harin, yayin da wasu da dama suka ɓace.


A safiyar ranar 28 ga Satumba, 2024, IDF ta bayyana cewa Nasrallah ya mutu a harin. Sa'o'i kaɗan bayan haka, Hezbollah da hukumomin Lebanon sun tabbatar da mutuwar Nasrallah.

Ma'anar Usulul-fikhi Da Ka'idar Shi

Ma'anar Usulul-fikhi Da Ka'idar Shi

Usulul-fiƙhi, usulul-fiƙhi yana nufin ƙa'idodi da dokokin da ake amfani da su wajen fitar da hukunce-hukuncen fiƙihu daga nassoshin Qur'ani da Hadisi.


Ma'anar Usulul-fikhi Da Ka'idar Shi
Hoto: Godofvecktor/Freepik

Marubuci:- Habeeb Awaisu Mmr


A taƙaice, usulul-fiƙhi shi ne tsarin da yake koyar da hanyoyin da malamai ke bi don su fahimci nassoshi da kuma fitar da hukunci daga cikinsu.


Don haka usulul-fiƙhi yana bayyana yadda ake fitar da hukunce-hukuncen ne.

Gajerun Sakonnin Soyayya Masu Taba Zuciyar Masoya

Gajerun Sakonnin Soyayya Masu Taba Zuciyar Masoya

Idan wani yana yabon ki sai na ji daɗi, kasancewar ki mai girma ce, sai kuma kishi da haushi su cika zuciyata domin dukkan yabon ki zai fi dacewa a ce ni nake furta su ba wani ba.


Sakonnin Soyayya Masu Taɓa Zuciyar Masoya
Hoto: Scme


Marubuci:- Muh'd Captain


Idan na ji an kira suna irin naki, sai na juya tunanina ke ce zan gani.


Zan kula da ke fiye da ma kaina, domin ke ce ni.


Zan ba ki farin ciki da komai nawa. Ina son ki kamar yadda nake son mahaifiyata.


Dukkan lokacina naki ne, tabbas na sani kuɗi ba zai ba ni ke ba, ina tausayawa kaina idan na rasa ki a rayuwa.


Mutum ba ya rayuwa dole sai da numfashi, ke ce numfashina.


Babbar ni'ima ce na samun mace kamar ki a cikin rayuwata.

Friday 27 September 2024

Karanta Addu'o'in Roƙon Ruwan Sama

Karanta Addu'o'in Roƙon Ruwan Sama

اَللَّهُمَّ اسْقِنَا غَيْثاً مُغِيثاً مَرِيئاً مُرِيعاً، نَافِعاً غَيْرَ ضَارٍ، عَاجِلاً غَيْرَ آجِل. 


Allahummas-qina ghaythan mugheethan maree-an muree'an, nafi'an, ghayra dar, 'ajilan ghayra ajil.


Addu'o'in roƙon ruwan sama
Hoto: Hyderabad water

Ya Allah! Ka shayar da mu ruwan sama mai yaye tsanani, mai daɗi, mai ni'ima, mai amfani ba mai cutarwa ba, da gaggawa ba da jinkiri ba.


اَللَّهُمَّ أغِثْنَا، اَللَّهُمَّ أغِثْنَا، اَللَّهُمَّ أغِثْنَا.


Allahumma aghithna, allahumma aghithna, allahumma aghithna.


Ya Allah! Ka yi mana agaji (da ruwan sama) Ya Allah! Ka yi mana agaji. Ya Allah! Ka yi mana gaji.


اَللَّهُمَّ اسْقِ عِبَادَكَ وَبَهَائِمَكَ، وَانْشُرْ رَحْمَتَكَ وَأَحْيِي بَلَدَكَ المَيِّتِ.

Allahummas-ki 'ibadak, wabaha-imak, wanshur rahmatak, wa-ahyi baladakal-mayyit.


Ya Allah! Ka shayar da bayinka, da dabbobinka; kuma ka yaɗa rahamarka, Ka rayar da ƙeƙasasshiyar ƙasarka.

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (2)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (2)

Ya juyo ya soma tafiya sannan ya waigo ya ce, "Wallahi ba domin kada ka ce na matsa maka ba da na ƙara maka wani saƙon. Muhimmi ne kwarai na mance da shi. Jakada ya ce, "to matso ka faɗa min!" Suka sake rankayawa yana ta faɗa masa saƙo. Haka suka yi ta yi har kafin su ankara sai ga shi sun isa garin da Laila take.


Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Layla
Hoto: Wikimedia Commons

Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Jakada ya yi mamakin irin wannan soyayya, sannan ya ce da Majnun, "Babu buƙatar kai wa Laila saƙo gare ni domin kuwa ga shi mun zo garin da take." Da jin haka Majnun ya cika da farin ciki da murna. Ya faɗi sumamme don tsananin farin ciki.


Bayan ya farfaɗo Jakada ya ce masa, “Ba na so a gan ka, domin jama’a na iya kama ka su yi maka wulaƙanci kafin ka ga Laila. Ga wani kango can ka shiga ka zauna a ciki ka huta domin ka yi tafiya mai yawa. Zan isar da saƙonka ga Laila yanzun nan.”


Majnun ya yarda da shawarar Jakada ya shiga kangon nan ya zauna zuciyarsa na harbawa kamar ta tsage. Sakamakon tafiyar da ya sha duk ya yi futu-futu. Tufafinsa sun yi jawur da ƙura, gashin kansa duk ya kukkulle, ga ƙafafunsa sun yi fato-fato da ƙura da faso da kaushi. Ga shi nan dai yarbajila da shi. Duk da haka, da ya tuna cewar yana garin da Laila ta ke gaba ɗaya sai ya ji ransa ya yi fari fat. Ya cika da murna da farin ciki, zuciyarsa ta cika da bege ya riƙa rera waƙa yana cewa:


Na aika saƙona wajen masoyiya.


Zuciyata da rayukana gaba ɗaya.


Na miƙa su dukansu wajenki gimbiya.


Ke ce tawa haƙiƙa na faɗi gaskiya.


Na sallama miki kaina lahira da duniya.


Daga nan sai gajiya ta kama shi, ya ji yana so ya kwanta. To amma sai ya riƙa tunanin shin a wanne ɓangare Laila take? Domin ba ya so ya kwanta inda ƙafarsa za ta riƙa kallon jihar da take domin a wajensa hakan cin amanar ƙauna ne. Zai iya shurinta bai sani ba. Ya tsaya yana tunani, shin tana gabas ne ko yamma ko kudu ko kuwa arewa? Duk inda ya sa kansa sai ya tuna ƙila a wannan ɓangaren take, sai ya yi maza ya sake waje.


Daga baya dai sai ya samo igiya ya ɗaura a ƙafarsa ya samu gini ya ɗaura ƙafar, ya zamana yana reto kamar jemage. A wannan yanayi kuma bai fasa rera mata waƙa ba yana cewa:


Hajjina da Umarata na wajenki.


Makka ta da Madina na su ne ganinki.


Baitil Mukdis a wurina murmushinki.


Arzikina duk ni dai na ga dariyarki.


Na sallama kaina gaba wurinki.


Ƙishir ruwa na damunsa amma babu ruwa a kurkusa, haka ya haƙura wutar bege na hura shi, tana ƙone masa sassan jiki da zuciya.


Jakada ya yi sallama ƙofar gidansu Laila ta fito, ya ce mata, "Na yi ƙoƙari da gaske domin na yi miki magana, game da masoyinki Majnun wanda ban taɓa ganin tamkarsa ba a fagen so." Ya kwashe labarin duk yadda suka yi ya faɗa mata. Sannan ya ƙara da cewa, "Yanzu haka na bar shi a bayan gari domin gudun kada a wulaƙanta shi idan jama'a suka gan shi." Da Laila ta ji haka sai tausayinsa ya kama ta. Ta tafi wajen uwar goyonta ta ce mata, "Me yake faruwa ga mutumin da ya yi tafiyar mil ɗari da ashirin a ƙasa ba tare da ya huta ba?"


Tsohuwa ta ce, "Wannan mutumin ba zai rayu ba mutuwa zai yi." Laila na jin haka sai ta ji ta shiga damuwa, ta sake ce mata, "babu wani magani?" 


"Magani ɗaya ne a sanina. Dole ya sha ruwan saman da aka ajiye shi aƙalla shekara ɗaya, kuma dole ruwan ya zamana maciji ya sha daga gare shi. Sannan ya ɗaura igiya a ƙafarsa ya zamana kansa na kallon ƙasa zuwa wani lokaci. Idan ya aikata hakan wataƙila zai tsira da ransa."


Da ta ji haka sai ta yi tagumi tana cewa, "Wannan magani akwai wahalar samu, kai ba ma zai yiwu ba." Ta ɗaga hannu sama tana roƙon Allah ta ce, "Ya Allah mai ƙulla soyayya, mai bayarwa mai hanawa ka taimaki Qays Majnun ya samu wannan magani." Ta shafa sannan ta yi ajiyar zuciya ta ce, "Soyayya ba ta da magani sai ita kanta."


Allah da ikonsa, Majnun na rataye da ƙafarsa a sama ga ƙishirwa na addabarsa sai ya kwance igiyar ya tafi neman ruwa. Bai samu ruwa ba sai wani tsohon kasko a wani lungu. Ya tarar da wani zabgegen maciji na shan ruwan. Ya kore shi sannan ya kafa kai ya shanye ruwan gaba ɗaya. Ya samu waje ya zauna yana waƙe-waƙensa.


Da gari ya waye Laila ta shirya abinci mai rai da lafiya ta kirawo kuyanga a ɓoye ta faɗa mata komai sannan ta nemi ta kai wa Majnun inda yake a bayan gari. Kuma ta ba ta saƙon a faɗa masa cewar ita ma tana nan tana ƙaunarsa kuma tana son ganinsa, amma da zarar ta samu dama za ta zo ta gan shi. Yayin da Kuyanga ta je wajen sai ta tarar da mutane biyu. Ɗaya ya haɗa kai da gwiwa kuma duk ya rame ga kansa nan duguzunzum, ɗayan kuma mai kiɓa jawur da shi, sai dai ya manyanta. Kuyangar ta dube su duka biyun ta ga babu wanda ya cancanci Laila ta so shi.


Ita kanta ma ta ji duk ba su kwanta mata a rai ba, balle kuma Laila. Duk da haka domin cika umarni sai ta ce, "a cikinku wane ne Majnun?" Mai kiɓar ne kaɗai ya ji sai ya taso wajenta ya ce, "Me ya faru?"


Sai ta nuna kwandon abinci ta ce, "cewa aka yi na kawo masa wannan daga Laila." Nan da nan ya karɓe abincin yana cewa "Ni ne Majnun." Ta faɗa masa saƙon Laila ya yi mata ɗan wasa haka sannan ya sa abinci a gaba ya cinye. Ya ragewa Majnun ɗan kaɗan.


Daga wannan rana kullum sai ta kawo masa abinci da saƙon baka, shi kuma sai ya cinye ya rage kaɗan domin Majnun. Kullum Laila kan tambayi Kuyanga, "Me ya ce ki faɗa min?" Sai Kuyanga ta ce, "Wai ya gode madalla da abinci."


Laila ta shiga kokwanto anya kuwa Majnun ɗinta ne? Bayan kwana uku dai da ta gaji sai ta ce da Kuyanga, "Yaya kika ga kamannin Majnun din?" Kuyanga ta ce, "Wani mai ƙiiba yana da saje da ƙasumba...ya manyanta..."


Farat Laila ta ce, "Wallahi ba shi ba ne, wannan Jakada ne wanda ya kawo min saƙonsa. Majnun ba tsoho ba ne kuma ba shi da ƙiba." Ta dubi Kuyanga ta ce, "Su nawa ne a wurin?" Kuyanga ta ce, "Su biyu ne." Laila ta yi ajiyar zuciya ta ce, "to yau ba za a kai abinci ba, amma zan sa ki musu wata jarrabawa domin mu gane Majnun na gaskiya." 


Ta ba ta wuƙa ta faɗa mata abin da za ta yi da ita.


Kuyanga ta tafi wajensu Majnun, ta tarar da Jakada na tsaye yana jiranta. Tana zuwa ya soma yi mata sannu da zuwa. Ya miƙa hannu da nufin ya karɓi gara, maimako haka sai ya ga ta fito da wata sharɓeɓiyar wuka. Ta ce, "Laila ba ta da lafiya, ana buƙatar jinin masoyinta kwalba ɗaya wanda da shi za a haɗa maganin. Shi ya sa na zo wajenka na ɗiba."


Yana ganin haka sai jikinsa ya kama rawa ya ce, "To ni dai ba masoyinta ba ne, kuma ba ni ne Majnun ba, gashi can a zaune." Ta wuce zuwa wajen Majnun ta faɗa masa kamar yadda ta faɗa wa Jakada. Yana jin haka ya karɓi wuƙar da hanzari, ya sumbace ta sannan ya ce, "Na gode wa Allah da ya ƙaddara cewa jinina ne zai warkar da ciwon masoyiyata." 


Ya darzaza wuƙar a hannunsa, maimakon jini ya zubo sai wajen kurum ya yi farat fat, alamar babu jini. Ya sake keta wani wajen, nan ma babu jinin saboda bai ci abinci ba ballantana a samu abin da ake buƙata. Da ya ga haka sai ya soka wuƙar a hammatarsa inda babbar jijiyar jini take, nan jinin ya riƙa ƙwarara. Ya tara ya miƙawa kuyangar wadda tuni tsoro da mamaki sun hana ta motsi. Yayin da ta koma gida ta shaida wa Laila irin abin mamakin da ta gani wajen Majnun, sai Laila ta yi ta kuka tana tausaya masa.


A cikin gari kuwa, labarin Majnun ya cika gari, sai aka samu wasu shaƙiyan matasa suka ɗauko kulake suka nufi inda yake. Tun daga nesa da Jakada ya hango su sai ya hau taguwarsa ya sulale ya bar Majnun yana waƙe-waƙensa yadda ya saba. Matasan na zuwa suka hau bugunsa suna shuri da naushi da yakushi. Suka ɗaure shi da igiya sannan suka tsaya daga nesa suna jifarsa. Da Laila ta ji labari sai ta sheƙo da gudu ta zo ta kare shi daga bugun mutane, ta riƙa zaginsu tana korarsu. Shi kuwa duk da yana ɗaure ga bugun da ya sha amma sai ya ji ransa ya yi fari fat da ganin abar begensa ya riƙa ambaton sunanta yana cewa:


Laila, Laila, Laila tawa ce.


Domin a kanki ne na haukace.


Wasu na kallona wai na karkace.


To amma fa yau na samu dace.


Da ganin haskenki ya masoyiya.


Iyayen Laila suka turo aka tafi da ita gida tana kuka. Da suka ga lamarin ya wuce saninsu sai suka yi shirin yin balaguro na wani lokacin domin a tsammaninsu idan suka tafi suka jima Majnun zai gaji da nemanta har ya saduda ya haƙura.


Suka shirya kaya suka tafi wani gari da ba su ambata ba, gudun kada ya ji ya bi su can. To amma kafin su tashi Laila ta rubuta takarda a ɓoye ta ba wa kuyangarta ta kai wa Majnun. Ya buɗe ya karanta cewar "Masoyina, bulaguro za mu yi wani gari mai nisa, haɗuwar mu za ta yi wuya anan. Idan za ka iya mu haɗu a zangon farko cikin sahara.".


Yana gama karantawa ya ce da kuyangar, "Ki gaishe ta da kyau da kyau, kuma ki faɗa mata cewar ina nan tafe."


DUBA WANNAN: Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (3)


Lokacin da su Laila suka sauka a zangon farko ta tafi ita da kuyangarta zuwa inda ta ce masa ya je za ta same shi.


A tsammaninta bai isa ya zo wurin ba a wannan lokacin..........


Za mu ci-gaba Insha Allah.

Thursday 26 September 2024

Abubuwa 10 Masu Kawo Nasara A Farkon Fara Sana'a

Abubuwa 10 Masu Kawo Nasara A Farkon Fara Sana'a

Mene ne marabar wanda yanzu haka a lokacin nan da nake wannan rubutun yake samun riba, yana mayar da canji cikin aljihu da ragowar ku waɗanda kullum za ku tashi daga bacci, sannan ku koma ku kwanta da dare ba tare da samun ko ƙwandala ba? Tsoro.


Abubuwa 10 Masu Kawo Nasara A Farkon Fara Sana'a
Hoto: Business News daily

MarubuciBello Galadanchi


Ko sau nawa mai son ya yi sana’a ya tabbatar wa kanshi abin da yake da niyyar yi.


Karanta waɗannan abubuwa goma da duk wani mai so ya fara sana’a yake tsoro da hanyar shawo kan su. 


1. RASHIN SANIN DAGA INDA ZA A FARA.


Yawancin masu so su fara sana’a, ba su san daga inda za su fara ba bayan yanke shawarar hada-hadar da suke son yi. Ka fara da neman wani wanda ya cimma sak irin burin da kake son cimmawa. 


Yi bincike akan wannan mutum, da irin kasuwancin sa sannan ka tuntuɓe shi ka gani ko zai iya ba ka shawara da bayanai. 


Idan ba shi da lokaci ko sha’awar ya yi maka magana, to za ka gane cewa ya samu nasara, kuma kai ma za ka iya. 


Ka ci-gaba da gashi sannan ka yi abun da ya fi mayar da hankali, kana ci-gaba da tafiya, hanyar na ƙara maka haske. 


2. RASHIN ƘWAREWA.


Ta yiwu ka san abubuwa da yawa akan hajar ka ko sana’ar ka domin amsa duk wasu tambayoyi da kwastomomi za su yi maka, da ma warware musu duk wasu matsaloli da ka iya tasowa. Saboda haka kar ka damu kanka idan kana ji kamar ba ka son komai a wannan fannin ba. 


Dangane da abubuwan da ba ka sani ba, za ka iya samo amsoshi. Babu kunya wajen neman ilimi. Maganar gaskiya, wannan abu ne ma da ya kamata ka ringa yi kullum idan kana so ka ci-gaba, komai girman sana’ar ka. Ba za ka taɓa daina koyo ba: Ka saka rigar ƙwararre sannan ka sadaukar da kanka wajen tabbatar da sana’a mai burgewa. 


3. ANA MAKA KALLON MARA HANKALI.


Mutane da yawa za su yi maka kallon mara hankali a lokacin da kake fara sabuwar sana’a, kuma gaskiya suka faɗa. 


Abu mafi sauƙi na yi shi ne kar ka taɓa ɗaukar kasada, ka je ka yi ta yi wa wani aiki har ƙarshen rayuwar ka. 


Ya ka ji a ranka dangane da abun da na rubuta yanzu? Saboda kai ɗan kasuwa ne, kuma kasada a cikin jinin ka take. Ba za ka iya rayuwa babu ita ba. 


Dole a yi maka kallon mara hankali mana a lokacin da za a ga ka fara abu ƙarami, kawai ka yi imani da baiwar da Allah Ya ba ka, kuma ka jawo hankulan ragowar mutane domin su ma su yi imani da shi. Ka rungumi rashin hankalin ka, kuma ka ƙaunace shi saboda waɗanda ake kira marasa hankali su ne suke yin arziki da suna a duniya.


4. RASHIN JARI.


Fara kasuwa zai yi matuƙar sauki idan duk wanda yake da shawara zai iya shiga cikin banki kai tsaye a ba shi kuɗi ko ya samu wanda zai ba shi jari. To saboda wannan duniyar ba mafarkin ka ba ne, mai so ya fara sana’a ba tare da jari ba, dolen dole su fara ko ta halin ƙaƙa. 


A farko ba ka da jarin da kake buƙata, nan bada jimawa ba za ka gane cewa farawa sannu a hankali ba tare da komai ba ya fi. 


Ni ma da ₦1,500 na fara a watan Maris ɗin 2016. 


5. BA A YARDA DA KAI BA.


Ko kana shakkar cewa mutane za su mayar da hankali akan sana’ar ka saboda takardun ka ko jinsin ka, ko launin fatar ka, kai dai ka ɗauki ciniki da muhimmanci sannan ka faranta wa kwastoman rai. 


Mutane za su iya yanke shawara saboda siffar ka, amma babu wanda zai gardama da ƙwarewa da hazaƙa. Ko a farko babu wanda ya yarda da kai, a hankali mutane za su fahimta kuma za su yi imani da yadda kake gamsar da duka kwastomomin ka. 


6. RASHIN SAMUN KWASTOMOMI.


Akwai matuƙar fargaba a lokacin da kake tallata wa duniya baiwar ka ko sana’ar ka a karo na farko, kana damuwa ko za a daraja ta ko saɓanin haka. Sai idan ka fara kasuwancin ka ne a lokacin da dama kana da mutane da yawa da suka san ka, kuma suka amince da kai shi ne za ka ga an fara ba ka kuɗi, idan ba haka ba, to wallahi ba za ji an cika maka inbox ko WhatsApp da saƙonni ba.


Idan ka tunkari kasuwanci cikin nishaɗi da raha, akai-akai kana cika alƙawura, to babu shakka za ka ga canji a ɗan lokaci. A halin yanzu, sai ka dage wajen tsara yadda za ka ringa yin talla, sannan ka yi nazari domin ƙara ƙwarewa wajen sanin sana’ar, kuma ka yi wa kanka adalci saboda ka kai inda jama’a da yawa ba su kai ba. 


7. RASHIN SANIN YADDA ZA KA RIƘE SANA’AR BAYAN KA YI NASARA.


Gazawar rashin samun ƙalubalen da kusan duka masu fara sana’a suke fuskanta shi ne gabatar da sana’ar da duniya ta daɗe tana jira. 


Yi tunanin da ka kawo kaya ko ka buɗe shago, mutane sun yi layi suna son ganin ka ko kayan ka. Shin wannan abun baya razana ka? Kana tsoron samun nasara ne, ko fargabar rashin iya biyawa kowa buƙata?


Ba kai kaɗai ba ne. Samun nasara na jawo kaɗaici, amma dole sai an samu wani a sama domin gabatar wa duniya abin da take buƙata. 


8. SAKA IYALINKA DA ‘YAN GIDAN KU A WANI HALI.


A lokacin da kake fargabar cewa wannan sabuwar sana’a ba za ta iya biya wa iyalanka buƙatun su ba, ko za a iya shan kunya, to idan wani ya gaya maka cewa iyalanka da ‘yan gidanku su ma suna buƙatar wannan horo domin ƙara danƙon zumunci da iyali? Matar ka ko mijin ki, ko iyaye na buƙatar ba ka kafaɗar hutawa. 


‘Ya’yan ka za su so su ga ka sayo wannan motar ko ka gina wannan gidan da kake ta so. Saboda haka ka yi wa iyalin ka magana, ka gaya musu me ka saka a gaba, kuma za ka yi ƙoƙari wajen tabbatar wa ba su wahala ba, ko ka bar su da yunwa. Ka gaya musu ɓaro-ɓaro irin kasada da haɗari dake cikin wannan sabuwar sana’a da muhimmancin zuba lokacin ka da ƙarfin ka domin cimma nasara. Ka shirya iyalanka ko ‘yan gidan ku yadda ya kamata sannan ka tambaye su su yi wannan tafiya da kai. 


9. KUƊAƊEN DA KAKE SAMU BA ZA MA SU BIYA UWAR JARIN DA AKA SAKA BA.


Shi fa ɗan kasuwa musamman mai fara sana’a shi ne mutumin da yake buga-buga da ɗaukar babbar kasada wanda ba kowa ne zai iya ba. 


Idan ka zuba uwar jari a cikin sana’a, kuma ba ka ga riba ta fara fitowa nan take ba, kawai ka ci-gaba da gashi. Idan har ka miƙa wuya kafin ka fara samun riba, to ba za ka taɓa samun riba ba. Idan kuma har ka yanke shawarar daina sana’ar kafin ka fara samun riba, to ka tuna cewa a baya ka samu jari, saboda haka za ka iya sake samowa. 


10. KOMAI BA YA TAFIYA YADDA YA KAMATA


Ko ƙaramin yaro ba ya kawai miƙewa ya fara tafiya lokaci ɗaya. To idan ya tashi, sannan ya faɗi me ya kamata ya yi? Ya zauna ya yi ta kuka? A'a, ya ƙara miƙewa sannan ya sake gwadawa. 


Miƙewa tsaye na daga cikin wannan harka. Idan matsaloli suka addabi sana’a, wannan kawai ya nuna cewa ka sake miƙewa ne ka ƙara gwadawa.


A matsayin ka na ɗan kasuwa, na tabbata za ka iya samun nasara, saboda haka kar rugujewar sana’a ta firgita ka. Za ka iya sake miƙewa ka gwada. 


Yanzu da ka gama karanta wannan rubutun, je ka yi abu ɗaya da ya fi maka amfani a wannan rubutun. 

Karanta Gajerun Kalaman Amsa Kiran Waya Na Soyayya

Karanta Gajerun Kalaman Amsa Kiran Waya Na Soyayya

Kowacce soyayya da kike gani tana samuwa ne a bisa wasu dalilai, saboda haka, ina son bayyana miki cewa, ina son ki ne saboda ke ce da ma wacce zuciyata ta daɗe tana jira, ina tare da ke a duk inda na shiga.


Gajerun Kalaman Amsa Kiran Waya Na Soyayya
Hoto: Photo done 



Ina son ki, ba na biɗar ganin wata idan ba ke ba. Ina alfahari da ke a rayuwa ta.


Matsayinki a gare ni, tamkar na wani dutse ne na musamman da yake jikin wani zobe, wanda ya kasance a dukkan lokacin da babu shi, zoben zai zamo mummuna mara daraja abin nunawa.


Ki kasance tare da ni masoyiya ta, ina son ki so mara misaltuwa domin ke ce wacce zuciyata ta ba wa yarda, kodayaushe burina ki kasance tare da ni.


Ina son kasancewa ne tare da wacce za ta kasance cikin saka ni farin ciki da walwala, ta sa ni murmushi a lokacin da nake cikin damuwa, wacce za ta kasance cikin so na a kowanne irin yanayi.


Na san babu wacce za ta iya hakan sai ke, a saboda haka nake ƙara bayyana miki cewa  ina son ki, son da babu iyakar shi.


Ina fatan zuciyata da taki su narke su zama abu guda har zuwa ƙarshen rayuwa.


Zan kasance cikin yi miki addu'ar samun nasara a dukkan al'amuranki,  kuma zan kasance cikin son ki har ƙarshen rayuwata.


Kalamai zuwa ga masoyiyar asali.